Gobara ta kashe aƙalla mutum 5 a Pakistan
Wuta gobara da ta tashi a wasu rukunin shaguna a birnin Karachi na Pakistan ta yi sanadin rasa rayukan aƙalla mutum biyar.
Gobarar ta tashi ne a rukunin shaguna na Gul Plaza a yammacin jiya Asabar da kuma har kawo yanzu ba a kammala kashe ta ba.
Jami'an kashe gobara sun ce tsananin zafin da kuma yadda wutar ke ci sosai suna na kawo cikas ga aikin ceton da ake kuma ana fargabar adadin waɗanda mutu zai iya ƙaruwa saboda akwai waɗanda suka maƙale a cikin shaguna.
Gobarar ta ginin na Gul Plaza mai ɗauke da shaguna sama da dubu ɗaya ta tashi ne da yammacin Asabar.
Wani mai magana da yawun hukumar bayar da agajin gaggawa ya shaidawa BBC cewa za a iya ɗaukar kwanaki kafin a iya kashe wutar.




