Odion Ighalo: Dan wasan Najeriya ya kawo karshen zamansa a Manchester United

Asalin hoton, Getty Images
Dan kwallon Najeriya, Odion Ighalo ya bayyana cewa 'mafarkinsa ya zo karshe' saboda zai bar Manchester United bayan shafe shekara daya yana murza leda a kulob din a matsayin aro.
Dan wasan, mai shekaru 31, ya zura kwallo biyar a wasa 23 da ya buga wa United tun bayan da aka dauko shi daga kungiyar Shanghai Shenhua ta China.
Ighalo ya ce: "Ina godiya da wannan damar kuma ba zan taba mantawa ba".
A sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter Ighalo ya ce " Zan ci gaba da kasancewa mai goyon bayan Manchester United har abada".
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
A kakar wasa ta bana, Ighalo ya murza leda ne kawai na minti tara a gasar firemiya kuma ya koma cin benci ne bayan da aka dauko Edinson Cavani a cikin watan Oktoba.






