KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 2 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Abdullahi Bello Diginza

  1. Trump ya yi gargaɗin samun ƙarin mutuwar dakarun Amurka a yaƙin Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya wallafa wani bidiyo a shafukan sada zumunta, sannan ya bayyana a wasu kafafen watsa labarai, inda ya shaida wa jama’ar Amurka cewa ya kamata su kasance cikin shirin yiwuwar samun karin mace macen dakarun ƙasar a yaƙin da suke yi da Iran.

    An tabbatar da mutuwar sojoji uku zuwa yanzu, yayin da wasu biyar suka samu munanan raunuka.

    Da yake magana da NBC, Trump ya ce hare haren da aka kai wa Iran sun zama dole, kuma za su iya shafe aƙalla wata guda.

    A wani saƙo da ya aika wa dakarun rundunar juyin-juya halin Iran, Mista Trump ya bukaci su yi saranda, ko su fuskanci mutuwa.

  2. Farashin mai ya tashi a kasuwanni duniya saboda yaƙin Iran

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Farashin ɗanyen mai ya tashi da kashi goma cikin ɗari yayin da kasuwannin makamashi a Asiya suka buɗe a ranar Litinin, ƙari mafi yawa da aka samu tsawon watanni.

    Wannan yana nuna haɗarin da ke tattare da jigilar mai ta Mashigin Hormuz da Iran ta ba da sanarwar rufewa.

    Tuni ƙasashen duniya suka fara shirin tunkarar sakamakon da ke tattare da hakan, la'kari da cewa ta nan ne ake wucewa da aƙalla kashi 20 cikin 100 na makamashin da ake amfani da shi a duniya ciki har da man fetur.

    Rahotanni sun ce dakarun sojin ruwan Iran na kai hari kan dukkan jiragen ruwan da suka nemi kangarewa umarninsu na ja da baya, harma sun lalata wasu jiragen dakon mai uku.

    Kasuwannin hannayen jari da suka buɗe da safiyar nan a Asiya sun fadi warwas. Akwai fargabar cewa rikicin da ke ci gaba da faruwa zai iya yin mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya.

  3. Hare-haren Isra’ila sun kashe aƙalla mutum 31 a Lebanon

    ....

    Hare-haren sama da Isra’ila ta kai kan Beirut da kudancin Lebanon sun kashe mutum 31 tare da jikkata 149, a cewar ma’aikatar lafiya ta ƙasar yayin da rikici ke ƙaruwa a Yankin Gabas ta Tsakiya

    Sanarwar ta ce adadin na wucin gadi ne kuma ana ci gaba da tantancewa.

    Babban hafsan rundunar sojin Isra’ila, Eyal Zamir, ya bayyana cewa sojojin sun fara wani farmaki da ya kira “gagarumin shiri” kan ƙungiyar Hezbollah wanda zai iya ɗaukar kwanaki da dama.

    Tashin hankalin yankin ya ƙaru ne sakamakon rikicin kashe jagaron addinin Iran Ayatollahi Khamenei a hare-haren da Isra'ila da Amurka suka kai Iran.

    Rikicin da ake ciki yanzu na ƙara tayar da hankalin ƙasashen duniya, musamman saboda fargabar cewa faɗa zai iya bazuwa zuwa cikakken yaƙi a yankin Gabas ta Tsakiya.

  4. Yadda Amurka da Isra'ila suka kwashe watanni suna kitsa kashe Ayatollah Khamenei

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Kisan da aka yi wa Jagoran Addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya faru ne da safe, ba da tsakar dare ba, kamar yadda wasu za su yi tsammani.

    Hakan ya faru ne saboda Amurka da Isra'ila sun yi amfani da wani bayanin sirri da ya zo musu ƴan awanni kafin lokacin.

    Tsawon watanni, Amurka da Isra'ila sun riƙa dakon lokacin da manyan jagororin Iran za su haɗu wuri ɗaya, daga nan sai suka fahimci cewa Khamenei zai halarci wani gida a tsakiyan birnin Tehran da safiyar ranar Asabar.

    Haka nan kuma sun gano wani wurin da manyan sojoji da jami'an tattara bayanan sirri suke yin wata ganawa a daidai wannan lokacin.

    Tsawon watanni, Amurka da Isra'ila sun riƙa bibiyar duk wani motsi na jagoran addinin na Iran.

    Hanyar da suka yi hakan abu ne na sirri, duk da dai shugaban Amurka Donald Trump ya ɗan bayar da satar amsa a bayanin da ya wallafa a shafin sada zumunta.

    "Ya gaza zulle wa bayananmu na sirri da kuma nagartaccen tsarin bibiyar da muka yi amfani da shi."

    Wannan zai iya zama mutum ne ke ba su bayanai ko kuma wata fasaha ta bibiyar jami'an Iran.

  5. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Litinin.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.