Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Qatar 2022: Kasashe 48 ne za su je gasar cin kofin duniya
Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya Fifa Gianni Infantino ya ce kasashe 48 ne za su halarci gasar cin kofin duniya wacce za a yi a kasar Qatar a shekarar 2022.
A baya an shirya fara amfani da tsarin kasashe 48 ne a shekarar 2026, inda kasashen Amurka da Canada da kuma Mexico za su karbi bakuncin gasar.
Kasashe 32 ne suka halarci gasar ta bana wadda aka yi a kasar Rasha.
Sai dai wannan sauyin zai tilasta wa Qatar ta hada gwiwa da wasu kasashe a yankin Gabas ta Tsakiya don karbar bakuncin gasar, a cewar shugaban hukumar.
"Idan abu ne da zai yi wu, to me ye zai hana mu?" in ji shi.
"Muna duba yiwuwar hakan, muna tattaunawa da abokanmu a Qatar da sauran kawayenmu da ke yankin kuma muna fatan hakan mai yiwuwa ne."
Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake magana a babban taron hukumar kwallo kafa ta nahiyar Asiya a sabuwar hedkwatar hukumar a birnin Kuala Lumpur a kasar Malaysia.
"Ina so a kara bai wa kowace kasa damar fafatawa a gasar," in ji shi.