Maiduguri: An kai harin kunar bakin wake

Asalin hoton, .
Rahotanni daga jihar Borno dake arewacin Najeriya sun ce wasu 'yan kurnar bakin wake da ake zargin 'yan Boko haram ne, sun kai hari a kauyen Mule dake wajen garin Maiduguri.
Lamarin dai ya auku ne a wurin binciken ababan hawa na jami'an tsaro.
Wasu mazauna garin sun ce, an samu asarar rayuka.
Kungiyar Boko Haram dai tana ci gaba da kai hare-hare a jihar Borno.
Koda cikin wannan makon kungiyar kare hakkin dan adam Amnesty ta ce, nuna takaici akan kisan da ake yi a rikicin na Boko Haram.







