Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 05/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis 5 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi da Muslim Muhammad Yusuf

  1. Isra'ila ta ci gaba da ruwan wuta a Lebanon

    Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare a Lebanon ciki har da wajen birnin Beruit inda nan ce cibiyar mayakan Hezbollah da Iran ke marawa baya.

    An kwashe dare ana jin karar ababen fashewa da makamai masu linzami. Isra'ila dai ta gargadi dubban mazauna kudancin Lebanon su koma arewa domin tsira da ransu.

    Rana Hammoud ta tsere daga kudanci zuwa arewacin birnin Sidon.

    Ta ce lamari ne mai tada hankali da firgitarwa amma babu yadda za ka yi dole ka fita, anan kudin haya ya yi tsada daki ciki da Falo dala dubu 15000 kudin shekara kuma dole ka biya nan take.

    Jami'ai a Lebanon sun ce akalla mutum dubu 80 ne suka tserewa muhallansu saboda harin na Amurka da Isra'ila

  2. Tarayyar Turai ta bayyana matuƙar damuwa kan yaƙin gabas ta tsakiya

    Babbar jami'ar diflomasiyya a Tarayyar Turai Kaja Kallas, ta ce kasashen yankin gabas ta tsakiya sun shaidawa jami'ai a Turai suna cikin damuwa kan barazanar yakin basasa a Iran.

    Kallas ta ce su kansu kasashen Turai na cikin wannan fargabar musamman ta tsaron tekun yankin, da kokarin ganin lamura sun daidaita a mashigar Hormuz.

    Tana magana ne gabannin taron ministocin harkokin wajen kasashen Turai da za su yi ta kafar bidiyo, kan halin da ake ciki a gabas ta tsakiya.

    A bangare guda kuma har yanzu Iran ba ta bayyana wanda zai gaji jagoran addinin kasar Marigayi Ayatollah Ali Khamna'i, da harin Isra'ila da Amurka ya hallaka a ranar asabar da ta wuce.

    Ba kuma a sanar da lokaci ko ranar da za a yi ma sa Janaza ba, bayan dagewar da hukumomin Iran suka sanar.

  3. Sojojin Isra’ila sun ce Iran ta sake harba makamai masu linzami zuwa ƙasar

    Rundunar sojin Isra'ila (IDF) ta ce Iran ta sake harba makamai masu linzami zuwa ƙasar.

    A wani saƙo da rundunar ta wallafa a shafukanta ta sada zumunta, ta ce dakarunta na aiki domin kakkaɓo makaman kafin su afka wa wuraren da suka nufa.

    Rundunar ta kuma ce an aika da gargaɗi ta wayoyin hannu ga mutane a wuraren da abin ya shafa domin su san halin da ake ciki.

    Hare-haren na zuwa ne yayin da rikici tsakanin Iran da Isra’ila ke ƙara tsananta, inda ɓangarorin biyu ke zargin juna da kaddamar da hare-hare a cikin ‘yan kwanakin nan.

  4. Azerbaijan ta sha alwashin mayar wa Iran martanin hari mai zafi

    Shugaba Ilham Aliyev, na Azerbaijan ya yi alkawarin maida martani bayan abin da ya kira harin ta'addanci da Iran ta kai kasar da jirage marassa matuka.

    Sai dai sojojin Iran sun musanta kai harin jirgi maras matuka a wata makaranta da ke kusa da filin jirgin saman Nakhchivan da ke yammacin Azerbaijan a kusa da iyakar kasar da Iran.

    Ministan harkokin wajen Azerbaijan Jeyhun Bayramov, ya yi allawadai da kai harin, ya kuma ce kasar na da 'yancin maida martani.

    Ya kuma bukaci ganin jakadan Iran a kasar domin tattaunawa kan batun. Akalla mutum 2 ne suka jikkata a harin.

    Wannan na zuwa ne bayan Iran ta kai hare-hare sansanin sojin Amurka da ke kasashen Bahrain da Qatar, da Oman, da Saudiyya da Jordan da Hadaddiyar daular rabawa, da Kuwait, ya yin da ake cikin shirin ko ta kwana a kasashen Irai da Syria.

  5. Iran ta jefa miyagun makamai da jirage marasa matuƙa kan Daular Larabawa

    Ma'aikatar tsaro ta Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta ce ta kakkaɓo tare da lalata wasu muggan makamai masu linzami guda 6 da jirage marasa matuƙa 131 da Iran ta harba mata a yau Alhamis.

    Sai dai ta ce makami mai linzami ɗaya da jirage marasa matuƙa shida sun sauka a cikin ƙasar.

    Ma'aikatar ta ce tun baya da yaƙin ya fara a ranar Asabar, ta kakkaɓo miyagun makamai masu linzami 196 kuma ta lalata wasu makamai masu linzami masu cin gajeren zango guda takwas.

    Ma'aikatar ta ce an kashe mutum uku yayi harin, ciki har da 'yan ƙasashen Pakistan, Nepal da Bangladesh.

    Gwamnatin ƙasar ta ƙara da cewa mutum 94 sun jikkata tun bayan fara yaƙin.

  6. Iran ta ce ta kai hari sansanin sojin Amurka a Kuwait

    Rundunar sojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar da kai hari a sansanin sojin Amurka da ke Kuwait.

    Rundunar sojin Iran ɗin ta ce, jirage marasa matuka na sojin ruwan ƙasar sun kai farmakin ne a ranar Alhamis a sansanin Amurka da ke Al-Adiri a Kuwait.

    Tun bayan fara yaƙin, Iran ta harba jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami a wurare daban-daban a ƙasashen da ke yankin Gulf ciki har da Bahrain, UAE, Qatar, da Kuwait.

  7. An sace mata 100 da kashe sojoji 9 a Borno

    Aƙalla mata da yara kusan 100 aka sace a harin da 'yan Boko Haram suka kai wani sansanin 'yan gudun hijira a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

    Rahotanni sun bayyana cewa an kashe sojoji 9 a harin da aka kai garin Ngoshe.

    'Yan Boko Haram sun cinnawa motoci da tankokin wuta tare da kwashe makamai da dama.

    Sun kuma kashe Limamin masallacin sansanin 'yan gudun hijirar kafin su yi awon gaba da mata da yaran.

    Wani dan majalisar yankin ya yi kira ga jami'an tsaro su kara kaimi a yankin da 'yan Boko Haram ke cin karensu babu babbaka.

  8. An zaɓi ɗan Rwanda a matsayin 'shugaban cocin Ingila na duniya'

    An naɗa ɗan ƙasar Rwanda Most Revd Laurent Mbanda, a matsayin sabon shugaban cocin Ingila na duniya a yayin taron mabiya ɗarikar Angalika na duniya wato Gafcon a birnin Abuja, Najeriya.

    Hakan na zuwa ne bayan wani sashe na mabiya dariƙar Angalika da suka ce ba su amince da shugabancin Babbar Bishop ɗin cocin Ingila ba suka gudanar da nasu taron.

    A yanzu za riƙa kiransa da Primus Inter Pares.

    Kafin naɗin nasa a wannan muƙamin, Mbanda shi ne babban limamin cocin Angalika da ke Rwanda, kuma an yi zaɓen ne cikin sirri a daren ranar Laraba, inda aka sanar da naɗin nasa a Alhamis.

    Cocin Angalika ya zama coci na uku mafi tarin mabiya addinin kirista a fadin duniya. Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da bai wuce mako uku ba da rantsar da Dame Sarah Mullally a matsayin sabuwar Bishop ta cocin Canterbury.

    Cocin Ingila bai ce komai ba game da sanarwar.

    Wannan zaɓen na daga cikin manyan abubuwan da suka faru a taron Gafcon karo na 26 a Abuja babban birnin Najeriya, inda ɗaruruwan malaman addinin kirista ke halarta daga sassan duniya ciki har da nahiyar Arewacin Amurka, Australia da Afrika

    Masu zaɓen sun bayyana cewa ba wai suna adawa da zaman mace a matsayin shugabar cocin Ingila ba ne, sai dai suna ganin shugabancin cocin na Ingila yana ƙoƙarin kawo wani sabon tsari da ya saɓa da koyarwar da aka bi a ɗarikar Angalika, kuma ba su cikin littafin Injila.

    Sakataren yaɗa labaran taron na Gafcon karo na 26, Justin Murff, ya faɗa wa manema labarai a ranar Laraba cewa, Gafcon ba wai wani sashe ba ne da ya ɓalle daga haɗin kan mabiya Angalika, sai dai cocin Ingilan ne ya ɓalle daga tsarin ɗariƙar, inda ya ƙara da cewa ƙofar tuba a buɗe take idan sun shirya sake haɗewa da uwar ƙungiyar.

  9. Firaministan Birtaniya Starmer zai yi bayani kan rikicin Gabas ta Tsakiya

    Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, zai gabatar da sabon bayani game da rikicin da ke ƙara tsananta a Gabas ta Tsakiya a wani taron manema labarai da za a yi a 10 Downing Street da misalin ƙarfe 14:00 na rana agogon GMT.

    Ana sa ran Starmer zai yi magana kan yadda gwamnatin Birtaniya ke kallon rikicin da ke gudana tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka.

    Rikicin ya ƙara tsanani bayan yayin da Iran da Isra’ila da Amurka ke ci gaba da ƙaddamar da hare-hare kan junansu.

    Rahotanni sun ce hare-haren sun kai ga tashin hankali a ƙasashe da dama na yankin.

    Ana sa ran jawabin da Starmer zai yi zai bayyana matakan da Birtaniya za ta ɗauka domin kare muradunta, da kuma kira ga bangarorin da ke rikicin da su kauce wa matakan da za su kara tayar da rikici a yankin

  10. Kotu ta wanke Abba Kyari kan zargin rashin bayyana kadadrori

    Babbar kotun tarayyar Najeriya ta sallami dakataccen mataimakin kwamishinan 'yansanda Abba Kyari, ta kuma wanke shi daga wasu zarge-zargen da ake masa.

    Mai shari'a James Omotosho ne ya yanke hukuncin kan zarge-zarge 23 da ake masa da suka shafi rashin bayyana kadarorinsa da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasar (NDLEA) ta shigar a kan sa.

    An gurfanar da DCP Abba Kyari tare da wasu 'yan'uwansa biyu, waɗanda ake zargin su da yin rantsuwar ƙarya domin yin rufa-rufa wajen ɓoye asalin mamallakin dukiyar.

    A yayin yanke hukuncin, mai shari'a Omotosho ya ce NDLEA ya kasa gabatar da gamsassun hujjojin da za su tabbatar da zargin da ake yi masa.

    Alƙalin ya bayyana cewa ana iya mallakar fili ta hanyar gado ko kyauta da sauran su.

  11. Majalisar dokokin Kano ta gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan Kano

    Majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam, bisa wasu zarge-zarge da aka gabatar a kansa a gaban majalisar, ranar Alhamis.

    Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Hussaini ne ya gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan kan zarge-zarge da suka haɗa da almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin da ya shugabanci wasu hukumomin gwamnati.

    A kan haka ne majalisar ta ce, kamar yadda doka ta tanada, ta yanke shawarar sanar da mataimakin gwamnan game da matakin da ta fara ɗauka na tsige shi.

    A watan Janairu ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki a matakin tarayya, daga jam'iyyar NNPP, wadda ya lashe zaɓe ƙarƙashin ta a shekarar 2023.

    Sai dai mataimakin nasa Aminu Abdulsalam bai bi shi zuwa jam'iyyar ta APC ba.

  12. Iran ta zargi Amurka da Isra'ila da kai hari kan fararen hula

    Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta zargi Amurka da Isra'ila da kai hari kan fararen hula da gangan.

    A wani bayani da kakakin gwamnatin Iran ɗin Esmaeil Baqaei ya fitar a shafin X, ya ce hare-haren "sun yi tasiri kan hada-hadar kasuwancin duniya, lamarin da ya haifar da hauhawar farashin makamashi tare da karya darajar kuɗinta, da karya tattalin arzikin jama'ar ƙasar".

    Ya ƙara da cewa: "Hauhawar farashin ya fi ƙamari ga Iraniyawa: ana yanka mutanenmu ba tare da tausayawa ba, kuma ana kai hari kan fararen hula da gangan domin ƙara jefa su cikin ƙunci da asarar rayuka."

    Shugaban Amurka Donald Trump dai ya ce yana fatan ganin ya lalata makami mai linzamin Iran da lalata duk wani yunƙurinta na mallakar makamin nukiliya.

  13. Bahrain ta ce ta lalata sama da makamai masu linzami 70 na Iran

    Bahrain ta ce tun bayan da Iran ta fara kai hari a ƙasar a ƙarshen mako, ta lalata makamai masu linzami 75 na Iran da jirage marasa matuƙa 123.

    Iran ta kai wa babban birnin Bahrain, Manama hare‑hare sau dayawa a cikin kwanaki shida da suka gabata.

    A wani bayani da ta walafa a shafin Instagram, rundunar tsaron Bahrain ta ce tana ci gaba da “fuskantar jerin hare‑haren da makamai masu linzami daga Iran kuma ta yi kira ga jama’a su zauna a gida sai idan akwai buƙatar fita.

    Rundunar ta ƙara da cewa amfani da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa kan farar hula “ƙeta ka’idojin ɗanadam na ƙasa da ƙasa ne” kuma yana zama barazana ga “lafiya da zaman lafiya a yankin”.

  14. Rana ta shida: Ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Iran da ƙasashen Amurka da Isra'ila

    Iran ta harba makamai masu linzami zuwa Isra’ila cikin dare yayin da hare‑haren sama a Gabas ta Tsakiya suka shiga rana ta shida.

    Amurka da Isra’ila sun ƙara tsananta hare‑haren bama‑bamai a kan Iran a jiya. Sojojin Isra’ila sun kuma kai hari a kudancin birnin Beirut, inda ake ganin a nan cibiyar ƙungiyar Hezbollah take, bayan sun gargaɗi mazauna yankin.

    An kunna ƙararrawar hare‑haren sama a biranen Tel Aviv da Jerusalem don gargaɗin zuwan makaman roka inda aka kuma ji fashe‑fashe yayin da ake kakkaɓo wasu makamai da ake harba wa.

    Ba a samu rahoton mutuwa ko jikkata nan take ba amma Isra’ila ta fara sassauta wasu takunkuman da ta ƙaƙabawa jama’a saboda raguwar yawan makaman da Iran ke harbawa.

    Wani kakakin sojojin Isra’ila ya ce matakan da suka ɗauka na kai hari kan wuraren ajiye makaman Iran da wuraren harba su sun fara yin tasiri.

    A Iran kuwa, an sake jin fashe‑fashe a babban birnin Tehran, yayin da Isra’ila ta kai sabbin hare‑haren sama da suka kashe mutane a Lebanon.

    Jami’an Lebanon sun ce fiye da mutane 80,000 sun rasa matsugunansu sakamakon sabon rikicin da ke tsakanin Isra’ila da Hezbollah.

  15. A shirye muke mu sasanta Iran da Amurka

    Shugaban Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, ya ce ƙasarsa a shirye take ta taka rawan gani wajen warware rikicin Gabas ta Tsakiya, bisa ga alhakin da take da shi na duniya kan batutuwa kamar rikici da sauyin yanayi da rashin daidaito da talauci, kamar yadda shafin yaɗa labarai mai zaman kansa The Citizen ya ruwaito.

    “Afirka ta Kudu na shirye a kodayaushe ta sasanta Iran da Amurka a kan rikicin da ke ƙara ta'azzara." in ji shugaban.

    “Idan wata dama ta samu ko kuma idan an buƙace mu,a shirye muke, mu na duniya ne, don haka za mu iya taka duk rawar da Majalisar Ɗinkin Duniya ke so mu taka.”

    Ramaphosa ya ƙara da cewa “mun fitar da sanarwa a fili cewa muna son a tsagaita wuta a yaƙin da ke faruwa tsakanin Iran da Isra'ila da Amurka, muna son wannan hauka ya ƙare,” inda ya yi kira ga tattaunawa sannan ya nuna cewa a shirye yake ya tattauna da shugaban Amurka, Donald Trump.

  16. Hare-haren Isra’ila sun lalata gine-gine a Beirut

    Sabbin hotuna sun nuna rugujewar gine-gine da lalacewar wurare a birnin Beirut, bayan hare-haren sama da Isra’ila ta kai.

    Kafofin labarai na Lebanon sun ruwaito daren jiya cewa mutum uku sun mutu yayin da wasu shida suka jikkata sakamakon hare-hare biyu a kusa da babban birnin.

    An kuma ruwaito wasu hare-hare a kudancin Beirut - yankin da ke ƙarkashin ikon Hezbollah - a safiyar yau.

    Isra’ila ta ce a baya ta kai hari kan “wurin bayar da umarni da dama na ƙungiyar ta’addanci Hezbollah”.

    A lokaci guda, kafofin labarai na gwamnatin Lebanon sun ruwaito cewa wani jirgin sama mara matuƙi na Isra’ila ya kai hari wani ɗaki a Beddawi da sansanin ‘yan gudun hijirar Falasdinu kusa da Tripoli, inda ya kashe babban jami’in Hamas, Wassim Atallah al-Ali, tare da matarsa.

    Sojojin Isra’ila (IDF) har yanzu ba su yi tsokaci kan lamarin ba.

  17. Iran ta kai wa jirgin dakon man Amurka hari

    Gidan talabijin na gwamnatin Iran ya ce dakarun jiragen ruwan yaƙin ƙasar ta harbi wani jirgin ɗakon man Amurka a safiyar yau a arewacin Bahar Rum.

    Dakarun juyin juya halin Iran IRGC sun ce jirgin ya “sha harbi da makami mai linzami a arewacin Bahar Rum” kuma “har yanzu yana ci da wuta”, a wata sanarwa da aka karanta a talabijin na gwamnatin.

    IRGC ta ce tana da “cikakken iko” da Kogin Hormuz, wanda ke haɗa Bahar Rum da Tekun Indiya.

    Majiyoyi masu zaman kansu ba dai basu tabbatar da lamarin ba amma kuma ƙungiyar Kasuwancin Jiragen Ruwa ta Biritaniya MTO ta tabbatar da harin.

  18. Hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniyar Tehran

    Ga wasu hotuna da ke nuna yadda Hayaƙi ya turnuƙe sararin samaniyar Tehran, babban birnin Iran.

  19. Amurka ta bayyana sojojinta na biyar da na shida da Iran ta kashe

    Ma’aikatar tsaron Amurka, Pentagon, ta bayyana sunayen sojojinta na biyar da na shida da suka mutu a harin da Iran ta kai a ƙasar Kuwait a farkon rikicin da ke gudana.

    Ma'aikatar ta ce soja na biyar da aka tabbatar da mutuwarsa shi ne Manjo Jeffrey O’Brien, wanda ya fito daga garin Waukee wanda aka tura aiki a Kuwait a shekarar 2019.

    Soja na shida da ya mutu a harin shi ne Robert M Marzan mai shekaru 54, wanda ya fito daga Sacramento.

    Sojojin Amurka sun mutu ne bayan wani harin jirgi mara matuki da aka kai a wani cibiyar umarni ta sojoji a yankin Port Shuaiba a ranar Lahadi.

    Tun da farko rundunar sojin Amurka ta bayyana cewa sojojinta uku ne suka mutu a harin. Sai dai daga baya jami’ai suka tabbatar a ranar Litinin cewa adadin ya ƙaru, bayan wani soja ya mutu sakamakon raunukan da ya samu, sannan aka sake gano gawarwaki biyu a cikin ɓaraguzan ginin.

    A cewar Amurka, jimillar sojojinta shida ne suka mutu a wannan harin da ake zargin Iran ta kai.

  20. Majalisar dattijan Amurka ta goyi bayan Trump kan yaƙin Iran

    Majalisar dattawan Amurka ta kada kuriar bayar da goyon baya ga matakin sojin da Shugaba Trump ya dauka kan Iran, inda kan 'yan majalisar ya rabu tsakanin 'yan jam'iyyarsa ta Republican da kuma 'yan hamayya na Democrat.

    Majalisar ta yi watsi da bukatar ƴan Democrat ta cewa lalle sai shugaban ya samu amincewar majalisun dokokin kasar kafin, kai duk wani hari.

    Yanzu hankali ya karkata zuwa ga majalisar wakilan kasar wadda ita ma za ta yi kuria a kan kudurin dokar a yau Alhamis.

    Masu goyon bayan shugaban sun kafe cewa yana yakin ne bisa ikon da doka ta ba shi. Da yake magana a fadarsa ta White House Shugaba Trump ya ce zuwa yanzu matakin sojin a kan Iran na nasara.