Iran ta kai wa jirgin dakon man Amurka hari

Asalin hoton, Getty Images
Gidan talabijin na gwamnatin Iran ya ce dakarun jiragen ruwan yaƙin ƙasar ta harbi wani jirgin ɗakon man Amurka a safiyar yau a arewacin Bahar Rum.
Dakarun juyin juya halin Iran IRGC sun ce jirgin ya “sha harbi da makami mai linzami a arewacin Bahar Rum” kuma “har yanzu yana ci da wuta”, a wata sanarwa da aka karanta a talabijin na gwamnatin.
IRGC ta ce tana da “cikakken iko” da Kogin Hormuz, wanda ke haɗa Bahar Rum da Tekun Indiya.
Majiyoyi masu zaman kansu ba dai basu tabbatar da lamarin ba amma kuma ƙungiyar Kasuwancin Jiragen Ruwa ta Biritaniya MTO ta tabbatar da harin.









