An kashe mutum 323 tare da garkuwa da 949 a Kaduna a bana

Nasir El-Rufa'i

Asalin hoton, Kaduna Govt

Wani rahoto da ma'aikatar tsaro da harkokin cikin gida ta jihar Kaduna ta fitar ya nuna cewa daga 1 ga watan Janairu zuwa 31 ga watan Maris na 2021 an kashe mutum 323 tare da yin garkuwa da mutum 949 a jihar.

Samuel Aruwan, Kwamishinan da ke kula da ma'aikatar ya bayyana cewa alƙaluman na nuna mutanen da suka rasa rayukansu sanadiyyar ayyukan ƴan bindiga da fashin daji da garkuwa da mutane da hare-haren ramuwa, ciki har da mahara da ƴan bindigar da jami'an tsaro suka kashe.

Sai dai ya ce bai haɗa da jami'an tsaro da suka mutu a bakin aiki ba.

Haka kuma, alƙaluman ba su haɗa da mutanen da suka rasu sanadiyyar haɗurran abubuwan hawa da kisan kai ba.

Mutanen da suka rasu

Rahoton ya nuna cewa cikin mutum 323 da suka rasu, 20 mata ne yayin da 11 daga cikinsu ƙananan yara ne da shekarunsu ba su kai 18 ba.

Haka kuma mutane 236 daga ciki sun fito ne daga yankin Kaduna ta Tsakiya - wato a ƙananan hukumomin Birnin Gwari da Giwa da Igabi da Chikun da Kajuru, sai duk cikinsu Birnin Gwari ke da mafi yawan mutanen da suka mutu, mutum 77.

Yankin Kaduna ta Kudu na da mutum 68 da suka rasa rayukansu kamar yadda rahoton ya bayyana yayin da Kaduna ta Arewa ke da mutum 19.

Mutanen da aka yi garkuwa da su

Rahoton ya bayyana cewa cikin mutum 949 da aka yi garkuwa da su, yankin Kaduna ta Tsakiya ne ya fi yawan mutanen inda aka yi awon gaba da mutum 782 a ƙananan hukumomin Birnin Gwari mai mutum 291 haka kuma Igabi na da mutum 227.

Sauran ƙananan hukumomi da aka fi garkuwa da mutane a jihar sun haɗa da Chikun (mutum 156) da Giwa (mutum 58) da Kajuru (mutum 46) duk a yankin Kaduna ta Tsakiya.

A yankin Kaduna ta Kudu an yi garkuwa da mutum 129 a cewar rahoton yayin da aka yi garkuwa da mutum 38 a yankin Kaduna ta Arewa.

Gaba ɗaya an yi garkuwa da maza 550 da mata 317 da ƙananan yara 82 a jihar a watanni ukun farko na wannan shekara.

Mutanen da suka samu raunuka

A ɓangaren mutanen da suka samu raunuka dalilin hare-haren da ayyukan ƴan bindiga da rikicin ɓangare a jihar, rahoton ya nuna cewa mutum 244 suka samu raunuka.

Daga cikinsu kuma 25 mata yayin da 6 ƙananan yara ne da shekarunsu ba su haura 18 ba.

A wani ɓangare na rahoton, an gano cewa an sace shanu 3,289 a faɗin jihar.

Nasir El-Rufa'i

Asalin hoton, Twitter/Kaduna_Gov

Me gwamnati ke yi game da batun tsaro a jihar a wannan shekarar?

Samuel Aruwan ya bayyana cewa gwamnatin jihar Kaduna ta samar da hanyoyi da take ganin za su fi dacewa wajen shawo kan ƙalubalen tsaro da ta ke fuskanta.

Ya ce gwamnati na ƙarfafa ayyukan leƙen asiri na cikin gida musamman a yankunan da matsalar tsaro ta fi ƙamari.

Haka kuma, tana taimakawa jami'an tsaron gwamnatin tarayya tare da ke aikin samar da zaman lafiya a jihar.

Rahoton Mista Aruwan ya bayyana cewa jihar Kaduna ta hanyar hukumar samar da zaman lafiya ta Kaduna State Peace Commission na tattaunawa da al'ummomi kan hanyoyin warware matsaloli cikin kwanciyar hankali mai makon ta hanyar daukar fansa.

Sannan ya ce akwai tsare-tsare da gwamnati ta samar musamman a yankunan da rashin tsaro ya fi tsauri kamar Birnin Gwari da Giwa da Igabi da Zaria inda ake zaton ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane na ɓuya.

Rahoton ya bayyana cewa akwai jami'an tsaro na musamman da aka tura Dajin Falgore da ke kan iyakar jihar Kaduna da jihar Kano wanda kuma ya yi ƙaurin suna a matsayin matattarar masu aikata manyan laifuka.

Rahoton ya bayyana cewa daga watan Janairu zuwa watan Maris kawai, an yi amfani da na'urori wajen ɗaukar bayanan jihar daga sama a ƙalla sau 150 don gano wuraren da ƴan bindiga suka fi aiki.

An kuma kai hare-hare ta sama a wuraren da aka gano su a Birnin Gwari da Giwa da Chikun da Kachia da ma wasu ɓangarorin jihar Neja mai maƙwabtaka.

Mista Aruwan, a cikin rahoton nasa ya ce kawo yanzu an kashe ƴan bindiga 64 a jihar.

Short presentational grey line

Jihar Kaduna dai na ɗaya daga cikin jihohin arewacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro ta ɓangaren garkuwa da mutane da ɓarayin daji.

Titin Kaduna zuwa Abuja da na Birnin Gwari na daga cikin hanyoyin da masu garkuwa da mutane suka fi addaba a jihar, kuma ana samun hare-haren daji a yankuna da dama a faɗin jihar.

A wannan shekarar kawai, an yi garkuwa da mutane ciki har da ɗalibai da dama daga makarantunsu kuma wannan na nema ya zama ruwan dare a jihar ta Kaduna.

A watan Maris, wasu 'ƴan bindiga suka shiga Kwalejin Koyon Aikin Gandun Daji a unguwar Afaka da ke jihar ta Kaduna suka yi awon gaba da ɗalibai sama da 30.

Ƴan kwanaki bayan haka ne kuma wasu maharan suka afka wa garin Rema a Ƙaramar Hukumar Birnin Gwari suka yi garkuwa da malama uku a wata makarantar firmare.

Sannan a farkon watan Afrilu har ila yau wasu ƴan bindiga sun shiga jami'ar Greenfield duk a Kaduna kuma suka tafi da wasu ɗalibai. Ƴan kwanaki bayan yin garkuwa da su ne maharan suka kashe ɗalibai biyar daga cikin waɗanda suka sace kuma suka yasar da gawarwakinsu a kusa da jami'ar.

Dama ko a shekarar da ta gabata ma, wasu mahara sun sace ɗalibai a Kwalejin Good Shepherd Major Seminary School a garin Kakau na jihar ta Kaduna.

Baya ga waɗannan an sha samun rahotannin ƴan bindiga su shiga gidajen mutane su yi garkuwa da su don kuɗin fansa kuma a wasu lokutan ma su yi kisa.

A yayin da jihar ke cikin wannan hali, gwamnan jihar Malam Nasir El-Rufa'i ya sha jaddada manufarsa ta cewa ba zai biya kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutane ba kuma ba zai yi sulhu ko ya tattauna da ƴan bindiga ba.

A cewarsa, yin sulhu da biyan kuɗin fansa na ƙarfafa wa masu laifin gwiwa, kuma wata dama ce a gare su ta ƙara sayen makamai.

Sai dai masana na ci gaba da fargaba kan ƙaruwar hare-hare da sauran matsalolin tsaro da suka riga suka mamaye jihar ta Kaduna.