Coronavirus: Mutum 65 ne suka kamu da cutar a Najeriya

A

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Cutar Coronavirus ta kashe fiye da mutum 3,000 a fadin duniya
Lokacin karatu: Minti 1

Hukumar hana yaduwar cutuka ta Najeriya ta ce mutum 65 aka tabbatar sun kamu da coronavirus a kasar.

A sakon da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Alhamis da daddare, hukumar ta yi bayani dalla-dalla game da jihohin da mutanen suka fito kamar haka:

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Lagos- 44

Abuja- 12

Ogun- 3

Ekiti- 1

Oyo- 1

Edo- 1

Bauchi-1

Osun-1

Rivers-1

Ta kara da cewa mutm uku sun warke daga cutar sannan mutum daya ya mutu.

Karin bayani kan coronavirus
Karin bayani kan coronavirus

Da ma gwamnatin kasar ta nuna matukar rashin jin dadinta game da yadda 'yan kasar suka ki yin biyayya ga umarnin da ta yi musu na daukar matakan kariya a kan cutar.

Ranar Alhamis, ministan watsa labaran kasar, Lai Mohammed, ya ce lokaci yana kurewa Najeriya a yunkurnta na dalike cutar.

Ya koka kan yadda masu cutar suke kin bayyanawa gwamnati gaskiyar hali da suke ciki da halin 'yan kasar na rashin yin tazara a mu'amalarsu da juna da kuma kin yin gwajin cutar.

A cewarsa, dole ne 'yan kasar su bi umarnin gwamnati idan ba haka ba a tursasa musu yin hakan.