WHO ta ayyana dokar ta baci kan Coronavirus

Annobar Coronavirus

Asalin hoton, Getty Images

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ayyana cutar coronavirus a matsayin babbar barazar lafiya a duniya.

Annobar cutar coronavirus wadda ta yi ajalin sama da mutum dari a kasar China na ci gaba da yaduwa a wasu kasashe.

''Babban dalilin shi ne abin da ke faruwa a wasu kasashe bayan China," inji babban jami'in WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus, a lokacin da yake sanar da 'yan jarida game da matakin a birnin Geneva.

Ya ce damuwar ita ce cutar na iya yaduwa zuwa kasashen da bangarensu na lafiya ke da rauni.

Mutum 170 annobar ta kashe a China ya zuwa yanzu.

Hukumar lafiya ta duniya ta ce mutum 98 sun kamu da cutar a wasu kasashe amma ba a samu mutuwa ba.

An samu mutum takwas da kamuwa da cutar daga wasu mutane a Jamus da Japan da Vietnam da Amurka.

Ghebreyesus ya kwatanta barkewar cutar a matsayin wanda ba a taba samun irinta ba, wanda kuma aka tunkara fiye da a kowane lokaci.

Ya yaba wa China bisa daukar manyan matakan hana yaduwar cutar.

Wakilin BBC na harkar lafiya James Gallagher ya ce a yanzu WHO za ta iya tallafa wa kasashe matalauta da masu matsakaicin tattalin arziki wajen karfafa sanya ido da suke yi a harkar lafiya, sannan da taimaka musu wajen shirin ko ta kwana.