KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 26/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 26 ga watan Fabrairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida

  1. Yau za a tantance yiwuwar cimma yarjejeniyar nukiliya tsakanin Amurka da Iran

    ...

    Asalin hoton, Reuters/ EPA

    A yau ne za a gudanar da zagaye na uku na tattaunawar da ake yi tsakanin Amurka da Iran a Geneva kan shirin makamin nukiliyar Tehran.

    Tattaunawar za ta tantance ko za a iya cimma wata yarjejeniya, inda Iran za ta iya haƙura da wasu daga cikin buƙatunta kan shirinta na nukiliya, ciki har da wasu ɓangarorin shirinta na Uranium.

    Ana kallon wannan tattaunawar da matukar muhimmanci, musamman yayin da Amurka ke ƙara karfin dakarunta a Gabas ta Tsakiya, mafi yawa tun bayan mamayar da ta kai wa Iraƙi a shekarar 2023.

    Iran itama ta ƙara karfafa shirinta domin tunkarar duk wani hari da ka iya zuwa.

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya ce tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan batun nukiliya, amma ya jaddada cewa yadda Iran ke dagewa kan cire batun makamai masu linzami shi ne babban ƙalubale a tattaunawar.

  2. Shin za a ci gaba da tsare El-Rufai har watan Afrilu, me doka ta ce?

    ....

    Asalin hoton, Kaduna State Government

    Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya shafe sama da kwana 10 a hannun hukumomin Najeriya.

    A ranar 16 ga watan Fabarairu ne El-Rufai, bisa raɗin kansa ya je ofishin hukumar yaƙi da rashawa da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa (EFCC), domin amsa gayyatar da hukumar ta yi masa.

    Tun a farko hukumar EFCC ta tsare shi har zuwa daren Laraba 18 ga watan Fabrairu kafin daga baya aka miƙa shi hannun hukumar yaƙi da almundahana da dukiyar al'umma ta Najeriya (ICPC), inda tun daga wancan lokaci har yanzu ba a ƙara jin ɗuriyarsa ba.

    Ko a ranar Laraba da hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya DSS ta gurfanar da tsohon gwamnan a kotu, ba a ga Malam El-Rufain ba, kasancewar hukumar ICPC ba ta kai shi kotun ba.

    A ranar Laraba babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dage ci gaba da sauraron karar da hukumar tsaron ta DSS ta shigar da El-Rufai game da zargin satar sauraron wayar mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.