An kashe mutum 12 a zanga-zangar Iran kan farashin fetur

Jami'ai a Iran sun ce an kashe mutum 12 a zanga-zangar kwana uku da aka yi wadda ta samo asali daga tashin gwauron zabi da farashin man fetur din kasar ya yi.

Birane da yawa sun gudanar da zanga-zangar inda suka rufe manyan tituna, suka kuma kai hari a bankuna da wasu gine-gine na gwamnati a wasu wuraren.

Hukumomi sun dakile hanyar sadarwa ta intanet domin rage yaduwar bayanai akan lamarin, a yanzu haka ba a iya cewa ga halin da ake ciki akan lamarin.

Sai dai, gwamnati na cewa, abubuwa sun yi sanyi.

Farashin man fetur ya tashi a daukacin Iran da kashi 50 bayan da aka janye tallafin man.

Dalilin yin haka a cewar gwamnati, shi ne don ta samu kudin da za ta tallafawa marasa karfi.

Dama Iran na fama da gurguncewar tattalin arziki saboda takunkumin da Amurka ta kakaba mata tun bayan da kasashen biyu su ka yi baram-baram kan shirin nukiliyar Iran.

Mutune biyu sun rasa rayukansu a garuruwan Sirjan da Behbahan kuma gwammai sun jikkata.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa an yi artabu da jami'an tsaro a lokacin da masu zanga zangar suka yi yunkurin kona wata ma'ajiyar man fetur a ranar Juma'a.

Wasu garuruwan da rikicin ya shafa sun hada da babban birnin kasar wato Tehran da Kermanshah da Isfahan da Tabriz da Karadj da Shiraz da Yazd da Boushehr da kuma Sari.

A yawancin biranen masu boren sun rufe hanyoyi ta yin amfani da ababen hawansu don rufe hanya.

Wasu hotunan bidiyo da aka wallafa a internet ya nuna wasu gine gine na ci da wuta da suka hada da bankuna.

Shugaba Hassan Rouhani ya bayyana cewa kashi 75 na yan kasar na cikin matsi, kuma karin farashin zi tafi ne kacokam kan tallafa musu don ganin sun samu saukin rayuwa.

Iran na daga cikin kasashen da ke samar da man fetur a duniya, kuma ta na sayar da man na ta da sauki sosai.

To sai dai takunkumin da Amurka ta kakaba mata ya dagula al'amura a kasar, da suka hada da kasa samun damar shigo da injinonan da mahakar man fetur din kasar ke bukata.

Bugu da kari, tattalin arzikin ta ya lalace, yayin da darajar kudin ta ta yi kasa,dalilian da suka haifar da hauhawar farashin ababen more rayuwa.