'Tabbas Adam Zango ya biya 46m domin karatun marayu'

Adam Zango

Asalin hoton, Instagram/Adam Zango

Bayanan hoto, Adam Zango ya biya wa 'yan makarantar sakandare miliyoyin naira don ci gaba da karatunsu
Lokacin karatu: Minti 1

Shugaban makarantar Professor Ango Abdullahi da ke birnin Zariya, Dr Shamsuddeen Aliyu Maiyasin, Garkuwar makarantar Zazzau, ya ce babu tantama kan naira miliyan 46 da fitaccen dan wasan Hausan nan, Adam Zango ya zuba a makarantar domin tallafa wa marayu 101 su yi karatu.

Dr Shamsuddeen ya kara da cewa ba wannan ne karon farko ba da fitaccen jarumin yake bayar da irin wannan gudunmawa ba ga marasa karfi musamman kan abin da ya shafi karatunsu.

Latsa wannan alamar lasifikar da ke kasa domin sauraron hirar Dr Shamsuddeen Aliyu da Haruna Ibrahim Kakangi.

Bayanan sautiDr Shamsuddeen Aliyu

A ranar Laraba ne dai Adam Zango ya wallafa batun tare da rasitin biyan kudin a shafinsa na Instagram.

Kauce wa Instagram
Ya kamata a bar bayanan Instagram?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a Instagram

Wannan batu ne dai ya janyo mahawara a kafafen sada zumunta, inda da dama ke ganin Adam Zango ba shi da kudin da zai iya biya wa marayu 101 kudin makaranta na shekara uku.

To sai dai BBC ta tuntubi wasu na kusa da jarumin inda suka shaida mata cewa "yana da gidauniya da ke neman tallafin mutane musamman masu hannu da shuni."