An sace dalibai mata shida a jihar Kaduna

Asalin hoton, Kaduna State Government
Wasu 'yan bindiga sun sace wasu dalibai mata su shida a makarantarsu a jihar Kaduna, kamar yadda rahotanni suka bayyana.
Bayanai sun ce an yi awon gaba har da malaman makarantar mai zaman kanta su biyu a lokacin da 'yan bindigar suka shiga makarantar a cikin daren Laraba.
Kwamishinan harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Mista Samuel Aruwan ya tabbatarwa da BBC faruwar al'amarin.
Mista Aruwan ya ce abin ya faru ne a makarantar Engravers College wadda take kauyen Kakau a karamar hukumar Chikun - makarantar tana da nisan kilomita 10 daga kamfanin mai na NNPC da ke Kaduna.
Har wa yau, Aruwan ya ce "sai bayan kammala bincike ne za a iya tabbatar da abin da ya faru."
Hazalika jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sanda a jihar DSP Yakubu Sabo ya ce jami'ansu sun bazama cikin daji domin neman "mutum takwas din da aka sace a makarantar."
Ya kuma ce maharan sun shiga makarantar ne ta bangaren da katangar makarantar da ta rushe.
"An tura jami'an tsaro makarantar domin kwantar wa da sauran dalibai hankali," in ji shi.










