MDD ta tsawaita aikinta na shiga tsakani a Libya

A truck firing a machinegun
Bayanan hoto, Wasu mayaka na harba bindigogi masu sarrafa kansu a Libya

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya tsawaita aikin hukumar da ke sa ido kan rikicin Libya wato UNSMIL na tsawon shekara daya saboda ta taimaka a kawo karshen yakin da ke neman mamaye dukkan sassan kasar.

Kwamitin ya nuna damuwarsa kan hare-haren da 'yan tawaye masu biyayya ga Janar Khalifa Haftar ke kai wa kan birnin Trabulus.

Majalisar DD ta sake nanata kiran da tayi a baya na dukkan bangarorin su cigaba da mutunta yarjejeniyar tsagaita wuta, kuma ta fadada ayukan UNSMIL na taimakawa an cimma wannan mataki.

Jakadan MDD a Libya Ghassan Salame, ya yi gargadin cewa kasar na iya afkawa cikin yaki gaba daya wanda ka iya janyo a raba ta gida biyu na din din din.

Ya kuma ce wasu kasashen waje ne ke rura wutar rikicin saboda yadda suke ba bangarorin kayan yaki - wanda ya sabawa takunkumin da MDD ta saka wa kasar kan batun.

Janar Khalifa Haftar, jagoran 'yan tawaye a Libya

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Janar Khalifa Haftar, jagoran 'yan tawaye a Libya

Jagoran 'yan tawaye, Janar Haftar na samun goyon bayan Faransa da Amurka da kuma Rasha.

Wannan kudurin na son ganin kasashen sun daina shisshigi cikin rikicin kasar.