Adam A. Zango ya yi hadari a Nijar

Asalin hoton, Others
Fitaccen jarumin fina-finan Hausa na Kannywood kuma mawaki, Adam A. Zango, ya yi hatsarin mota.
Zango yana tafiya ne a kan hanyarsa ta dawowa daga Jamhuriyar Nijar tare da wasu abokansa, kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Instagram.
Sai dai jarumin ya ce "Allah Ya kare su, domin hadarin ya tsaya ne kawai a kan motar da suke tafiya a ciki".
Zango yana yawan yin tafiye-tafiye musamman a lokutan bukukuwan sallah, inda ake gayyatarsa domin yin casu.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a Instagram, 1
BBC ta yi kokarin tuntubar A Zango domin neman karin bayani kan lamarin amma bai amsa wayar ba kawo yanzu.
Amma bayanai a shafinsa na Instagram sun nuna cewa ya je Niyami, babban birnin Nijar, domin yin wasan sallah.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da Instagram suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta Instagram da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a Instagram, 2
Ana dai yawan samun hadari a kan hanyoyin Najeriya musamman a lokutan bukukuwan Sallah ko Kirsimeti.
Masu lura da al'amura na alakanta hakan da rashin kyawun hanyoyi da kuma tukin ganganci daga bangaren wasu matafiyan.











