Buhari ya fitar da sunayen sabbin ministocinsa

Sadiya Farouk

Asalin hoton, Sadiya Farouk Twitter

Shugaba Muhammadu Buhari ya fara fitar da sunayen sabbin ministocinsa.

Bakwai daga cikin ministocin mata ne, kashi 16% kenan wanda kasa da kashi 35% ne da masu fafutika ke bukatar gani a cikin gwamnatin.

Mai bai wa shugaban shawara kan harkokin sada zumunta Bashir Ahmad ne ya fara wallafa sunayen a sahafinsa na Twitter a ranar Talata.

Daga cikin sunayen da aka fitar zuwa yanzu akwai tsofafin minsitocinsa akwai kuma sunayen sabbin mutane da a baya ba sa cikin majalisar zartarwar shugaban.

Tuni dai shugaban kasar ya aike sunayen ga majalisar dattijai domin tantancewa.

Sunayen sababbin ministoci a karon farko

  • Sheikh Isa Ali Pantami - Gombe
  • Sanata Godswill Akpabio - Akwa Ibom
  • Alhaji Sabo Nanono - Kano
  • Gbemi Saraki (Kanwar tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki) - Kwara
  • Rauf Aregbesola tsohon gwamnan - Osun
  • George Akume - tsohon gwamnan - Benue
  • Timipre Sylva - tsohon gwamnan - Bayelsa
  • Sadiya Farouk - Zamfara
  • Maryam Katagum - Bauchi
  • Ramatu Tijjani - Kogi
  • Sanata Olorunnibe Mamora - Legas
  • Sunday Dare - Oyo
  • Festus Keyamo - Delta
  • Sharon Ikeazor - Anambra
  • Sanata Tayo Alasoadura - Ondo
  • Pauline Tallen - Filato
  • Mustapha Buba Jedi Agba -
  • Olamilekan Adegbite - Ogun
  • Mohammed Dangyadi - Sokoto
  • Abubakar Aliyu - Yobe
  • Sale Mamman - Taraba
  • Muhammed Mamood - Kaduna
  • Uce Ogar - Abia
  • Emeka Nwajuiba - Imo
  • Akpa Udo
  • Clement Abam
  • Zubair Dada
  • Adeniyi Adebayo - Ekiti
  • Mohammed Abdullahi
  • Osagie Ehenere
  • Bashir Salihi Magashi - Kano

Tsoffin ministocin da suka dawo

  • Babatunde Fashola - Tsohon Ministan Ayyuka da Gidaje
  • Rotimi Amaechi - Tsohon Ministan Sufuri
  • Ogbonnaya Onu - Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha
  • Adamu Adamu - Tsohon Ministan Ilimi
  • Sanata Chris Ngige - Tsohon Ministan Kwadago H
  • Hadi Sirika - Tsohon Karamin Ministan Sufurin Jiragen Sama
  • Zainab Ahmad - Tsohuwar Ministar Kudi
  • Lai Mohammed - Tsohon Ministan Watsa Labarai
  • Musa Bello - Tsohon Minsitan Abuja
  • Abubakar Malami - Tsohon Ministan Shari'a
  • Sulaiman Adamu - Tsohon ministan ruwa
  • Baba Shehuri - Borno