INEC za ta ci gaba da zabe

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar zabe ta kasa INEC za ta ci gaba da zabe a wasu mazabu inda zaben bai samu kammaluwa ba.
Hukumar ta sanar da haka ne a wani bayani da ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta ce ta yi nazari kan yadda babban zaben ya gudana a kasa baki daya.
INEC ta kara da cewa ta yanke shawara kan zaben Sanata mai wakiltar Jihar Imo ta Arewa, inda bayan tattaunawa da karatun-ta-nutsu ta kafa kwamiti da zai duba zarge-zargen rashin adalci game da zaben da aka gudanar a ranar 23 ga watan Fabarairu.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Sannan kuma zai duba ko an bi ka'idojin da hukumar ta tanadar wajen gudanar da zabuka ko kuma a'a.
Kwamitin zai gabatar da rahotonsa a ranar 10 ga watan Afrilu.
Akwai kuma sauran wurare hudu da hukumar ta ce za ta sake zaben a cikinsu a ranar Asabar 13 ga watan Afrilu.

Asalin hoton, IINEC Nigeria
INEC ta kuma gode wa jami'an tsaro da jam'iyyu da kuma masu sa-ido na cikin gida da na waje, da ma jama'ar jihar Ribas, bisa rawar da suka taka wajen kammaluwar zaben.







