INEC za ta ci gaba da zabe

INEC Chairkman

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Hukumar zabe ta gode wa jami'an tsaro da masu sa-ido bisa rawar da suka taka
Lokacin karatu: Minti 1

Hukumar zabe ta kasa INEC za ta ci gaba da zabe a wasu mazabu inda zaben bai samu kammaluwa ba.

Hukumar ta sanar da haka ne a wani bayani da ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta ce ta yi nazari kan yadda babban zaben ya gudana a kasa baki daya.

INEC ta kara da cewa ta yanke shawara kan zaben Sanata mai wakiltar Jihar Imo ta Arewa, inda bayan tattaunawa da karatun-ta-nutsu ta kafa kwamiti da zai duba zarge-zargen rashin adalci game da zaben da aka gudanar a ranar 23 ga watan Fabarairu.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Sannan kuma zai duba ko an bi ka'idojin da hukumar ta tanadar wajen gudanar da zabuka ko kuma a'a.

Kwamitin zai gabatar da rahotonsa a ranar 10 ga watan Afrilu.

Akwai kuma sauran wurare hudu da hukumar ta ce za ta sake zaben a cikinsu a ranar Asabar 13 ga watan Afrilu.

INEC time table

Asalin hoton, IINEC Nigeria

Bayanan hoto, Jadawalin sake zabe

INEC ta kuma gode wa jami'an tsaro da jam'iyyu da kuma masu sa-ido na cikin gida da na waje, da ma jama'ar jihar Ribas, bisa rawar da suka taka wajen kammaluwar zaben.