INEC ta fasa ba 'yan takara shaidar cin zabe a Zamfara

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar zabe ta kasa INEC ta dakatar da bai wa 'yan takara da suka yi nasara a zaben gwamna da na 'yan majalisar jiha a jihar Zamfara takardar shaidar nasarar cin zaben, wato Certificate of Return.
Wannan ya biyo bayan wani umarni ne da hukumar ta ce ta samu daga wata kotu a birnin Sokoto game da rikicin jam'iyyar APC da ke da alaka yadda aka yi zaben fitar da gwanin da suka yi mata takara a jihar.
Hukumar ta bayyana haka ne a shafinta na Twitter, inda ta ce tana ci gaba da nazari kan umarnin kotun.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Tun farko dai INEC din ta sanya ranar Laraba 27 ga watan Maris a matsayin ranar da za ta gabatar wa da dan takarar APC Alhaji Mukhtar Shehu Idris shaidar lashe zaben gwamna da kuma 'yan majalisar jiha da suka yi nasara a zaben da aka kammala.
Yanzu dai hukumar ta ce ta dage bai wa 'yan takarar shaidar, har sai wani lokaci nan gaba da ba ta bayyana ba.
Jam'iyyar APC dai a jihar Zamfara na fama da rikici tun bayan zaben fitar da gwani da ta gudanar kafin babban zaben da aka gudanar a Najeriya.
A ranar Litinin ne wata kotu ta soke hukuncin wata kotun daban a kan 'yan takarar APC din na jihar.







