
Wasu da ake zargin 'yan Boko Haram ne suka kai hari a makarantar sakandaren mata ta kwana a Dapchi jihar Yobe da ke arewa maso yammacin Najeriya.
'Yan Najeriya sun yi ta murna da farin ciki sakamakon sako 'yan matan makarantar sakandaren Dapchi da Boko Haram ta sace, ta kuma dawo da su ranar 21 ga watan Maris.
An mayar da yaran garinsu ne a ranar Laraba da misalin karfe 3 na tsakar dare.
Sai dai har yanzu akwai sauran yarinya daya mai suna Leah Sharibu, da mayakan kungiyar ba su mayar da ita ba, tana hannunsu.
Amma kuna da labarin duk abun da ya faru tun farkon lamarin?
Kuna iya duba wannan kalandar da ke kasa tare da ci gaba da latsa gaba don samun cikkkun labarai da rahotannin yadda abubuwa suka yi ta wakana.