Mufti Menk ya taya Buhari murnar lashe zaben 2019

Getty Images

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Malamin ya taba ziyartar Shugaba Buhari a Abuja a shekarar 2018
Lokacin karatu: Minti 1

Shahararren malamin addinin Musuluncin nan Mufti Menk ya taya Shugaba Buhari murnar lashe zaben 2019.

Malamin wanda dan asalin kasar Zimbabwe ne ya yi fatan Allah "ya kare shugaban, ya kuma ci gaba da yi masa jagora a dukkan al'amuransa."

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

A ranar Larabe ne aka bayyana Shugaba Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben Najeriya a karo na biyu, abin da zai ba shi damar sake mulkar kasar na karin shekaru hudu masu zuwa.

Shugaban mai shekara 76, na jam'iyyar APC, ya kayar da tsohon Mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar, da tazarar kuri'u kusan miliyan hudu.

Sai dai jam'iyyar adawa ta PDP, wacce Atiku ya yi wa takara, ta yi watsi da sakamakon zaben da Shugaban Hukumar Zabe ta INEC Mahmood Yakubu ya bayyana da misalin karfe 4.30 na asuba.