2019: Buhari na jiran tabbatar ma sa da nasararsa

Shugaba Buhari

Asalin hoton, Presidency

Bayanan hoto, A shekarar 2015 aka fara zabar Shugaba Buhari bayan da ya kayar da shugaba mai ci a lokacin, Goodluck Jonathan, na PDP

Shugaban Najeriya mai ci Muhammadu Buhari na Jam'iyyar APC na jiran tabbatar da nasarar sake lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar ranar Asabar.

Sakamakon jihohi 36 da aka bayyana ya nuna Buhari ya ba babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP Atiku Abubakar ratar kuri'a sama da miliyan hudu.

Zuwa yanzu Atiku yana da yawan kuri'a 11,262,978, bayan kammala tattara sakamakon dukkanin jihohin Najeriya.

Tuni dai jam'iyyar PDP ta yi watsi da sakamakon, wanda ta kira aringizon kuri'u saboda ya saba wa sakamakon da tattara daga wakilanta.

Sai dai jam'iyyar APC mai mulki ta yi Allah-wadai da matakin da PDPn ta dauka.

A shekarar 2015 aka fara zabar Shugaba Buhari bayan da ya kayar da shugaba mai ci a lokacin, Goodluck Jonathan, na PDP.

Jam'iyyar ta PDP ta shafe shekara 16 tana da mulkar Najeriya.

Kuma Buhari ne ya zamo dan siyasar adawa na farko da ya lashe zabe a kasar.

Yaya zaben yake aiki?

Taswirar Najeriya
Bayanan hoto, Jihohin da APC da PDP suka lashe a taswirar Najeriya

Dan takarar da ya fi samun kuri'u ake ayyanawa a wanda ya yi nasara a zagayen farko, in dai har ya samu kashi 25 cikin 100 na kuri'un da aka kada a kashi biyu cikin uku na jihohin kasar.

'Yan takarar shugaban kasa 73 ne suka yi rijista, amma an fi yin gwagwarmaya ne tsakanin Buhari da Atiku.

Dukkansu sun fito ne daga arewacin kasar inda Musulmai suka fi yawa, kuma dukkansu sun haura shekara 70, yayin da mafi yawan 'yan kasar da suka yi rijistar zabe 'yan kasa da shekara 35 ne.

Bayanan 'yan takarar shugaban kasa a 2019

Ga bayanan wasu 'yan takarar
  • Jam'iyya
    Peoples Democratic Party (PDP)
    Ranar haihuwa
    25 ga watan Nuwamba 1946, Jada, Jihar Adamawa
    Tarihi
    • Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya a 1999 - 2007
    • Ya nema kuma an ka da shi kujerar shugban kasa a 2007 a jam'iyyar AC
    • A 1998 an zabe shi gwamnan jihar Adamawa. Kafin a rantsar da shi ne PDP ta dauke shi a matsayin mataimakin shugaban kasa ga Olusegun Obasanjo inda suka ci zaben a 1999, an rantsar da Atiku a ranar 29 ga watan Mayu na 1999 a matsayin zababben mataimakin shugaban kasa.
    • Ya nemi kujerar gwamnan jihar Gongola ta da (wadda yanzu take (Adamawa da Taraba) a 1991, inda aka ka da shi.
    • Jami'in Kastam na tsawon shekara 25. 1964 - 1989
  • Jam'iyya
    Alliance for New Nigeria (AN)
    Ranar haihuwa
    12 ga watan Mayu na 1971, Ibadan, Jihar Oyo
    Tarihi
    • Kwararre a kan harkar kasuwanci da jawabi
    • Yana koyar da shugabannin kamfanoni da ke aiki a nahiyar Afirka da shugabanci a jami'ar Standford
    • Shi ne shugaban kamfanin Gemstone na gogar da mutane a kan shugabanci,
  • Jam'iyya
    Young Progressive Party (YPP)
    Ranar haihuwa
    7 ga watan Mayu na 1963 a jihar Legas
    Tarihi
    • Lawya kuma masanin tattalin arziki
    • Tsohon mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya daga 2009 zuwa 2014, kuma mamba kwamitin kula da kudi
    • Moghalu tsohon jami'i ne a hukumar kula da harkokin wanzar da zaman lafiya na Maja;loisar Dinlkin Duniya dake a New York daga 1996 - 1997.
    • Tsohon jami'i mai ba da shawara kan harkokin shari'a na kotun majalisar dinkin duniya a kan Rwanda a 1997, daga baya aka yi masa karin girma zuwa jami'i mai hudda da jama'a na koyun.
    • Shi ne tsohon shugaban Global Partnerships and Resource Mobilization a hukumar kula da lafiya ta duniya
  • Jam'iyya
    Jam'iyyar APC
    Ranar haihuwa
    17 ga watan Disamba 1942, Daura, Katsina
    Tarihi
    • Shugaban kasa daga 2015 zuwa yanzu
    • Ciyaman din PTF, 1994
    • Tsohon shugaban kasa, 31 ga watan Disamba zuwa 27 ga watan 1985
    • Ya nemi kujerar shugaban kasa a 2003
    • Dan takarar jam'iyyar CPC a 2011 inda Jonathan na PDP ya ka da shi
    • Ministan Mai da Ma'adanai a 1976
    • Gwamnan Jihar Borno Fabrairu - Maris 1976
    • Gwamnan Arewa maso gabashin Najeriya a 1975 - 1976
  • Jam'iyya
    African Democratic Congress (ADC)
    Ranar haihuwa
    24 ga watan Disamba na 1956 a Randa, Sanga, Jihar Kaduna.
    Tarihi
    • Masanin tattalin arziki, Ma'aikacin banki, masani kan ci gaban kasa-da-kasa
    • Mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya a 2005 - 2007
    • Tsohon mai taimakawa tsohon shugaban kasa Jonathan a kan tattalin arziki da tsarin lamurra, mamba na kwamitin gudanar da tattalin arziki, kuma jami'i a bankin ci gaban Afirka.
  • Jam'iyya
    Allied COngress Party of Nigeria (ACPN)
    Ranar haihuwa
    28 ga watan Afrillu na 1963, jihar Anambara.
    Tarihi
    • Akawu kuma masaniyar tattalin arziki
    • Tsohuwar mataimakin Babban Bankin Duniya sashen Afirka 2007 - 2012
    • Ministar Ma'adanai 2005 - 2006
    • Ministar Ilimi a 2006 - 2007.
    • Wadda sunanta ya shiga jerin wadanda ake neman tantancewa na kyautar Nobel a 2018
    • Wadda ta assasa kungiyar yaki da rashawa ta duniya da kuma gangamin Bring Back Our Girls
  • Jam'iyya
    African Action Congress (AAC)
    Ranar haihuwa
    An haife shi a ranar 16 ga watan Fabrairun 1971 a Kiribi, jihar Ondo.
    Tarihi
    • Dan jarida, dan gwagwarmaya
    • Shi ne ya assasa jaridar yanar gizo ta Sahara Reporters a 2006, domin nuna al'adun Afirka da yaki da rashawa
    • Shugaban dalibai a jami'ar Legas

Tsari

Tsarin zabar 'yan takarar shugaban kasa an yi shi ne akan wadannan:
  • Jam'iyyu a majalisa
  • Sanannun jam'iyyu (masu dan takara wanda ba sananne ba)
  • Sanannun 'yan takara a jam'iyyu wadanda ba sanannu ba
  • Sananne a duniya yada labarai
  • Sananne a duniyar shafukan sada zumunta

Mai hoton

Getty, www.fela2019.com, atiku.org, tobuildanation.com, facebook, sowore2019.org

Wadanda suka hada wannan aiki

Shiryawa: Olawale Malomo. Bincike: Nkechi Ogbonna

Wadanne ne manyan batutuwan?

Najeriya ce kasar da ta fi kowacce arzikin man fetur a Afirka, amma cin hanci da gazawa wajen zuba jari ya sa abun da ake samu daga arzikin ya jawo matukar ci baya.

Farfadowar da har yanzu kasar ke yi daga koma bayan da tattalin arzikinta ya samu a 2016 na nufin babu isassun ayyukan yi ga dumbin matasan da ke fafutukar neman aiki.

Kusan kashi daya bisa hudu na matasan kasar ba su da aikin yi.

Presentational grey line

Zaben cikin alkalumma

  • Masu katin zabe mutum miliyan
  • Kashi 51 cikin 100 na masu kada kuri'a 'yan kasa da shekara 35
  • 'Yan takarar shugaban kasa 73 ne
  • Rumfunan zabe 120,000