An sako tagwayen da aka sace a Zamfara

Masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara sun sako 'yan matan nan tagwaye da suka sace a watan jiya.
Dangin tagwayen da kuma wani babban jami'i a Karamar Hukumar Zurmi daga inda aka dauke su, sun tabbatar wa BBC da sakin nasu.
Kuma sun ce suna cikin koshin lafiya.
Sai dai kuma sun ce ba a sako yayarsu ba - wacce aka kama su tare a wani gida da ke garin Dauran a watan jiya a yayin da suka je rabon katin bikin aurensu.

Karin bayani game da Zamfara:

- Kashi 67.5 ke rayuwa cikin talauci
- Iya karatu da rubutu: Kashi 54.7
- Take: Noma tushen arzikinmu
- Yawancin mutanen jihar manoma ne daga Hausa Fulani
- Yawan jama'a: Miliyan hudu da rabi (Alkalumman shekarar 2016)
- Musulmi ne mafi yawa
- Jihar da aka fara kaddamar da Shari'a - a 2000
Madogara: Shafin alkalumma na Najeriya.
Karanta karin wasu labarai masu alaka:








