Paul Pogba: Kocin Man Utd Ole Gunnar Solskjaer yana so ɗan wasan ya nuna jagoranci a filin wasa

Paul Pogba (left) and Manchester United manager Ole Gunnar Solksjaer

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Paul Pogba (hagu) bai buga wa Manchester United wasa ba tun ranar 26 ga watan Disamba
    • Marubuci, Daga Simon Stone
    • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Sport

Kocin Manchester United Ole Gunnar Solskjaer yana so ya ga Paul Pogba yana shugabanci a filin wasa.

Sau biyu kawai dan wasan mai shekara 27 ya buga wa kungiyar wasa tun daga watan Satumba saboda karayar da ya yi a kafa.

Kuma duk da rade-radin da ake yi kan rashin tabbacin makomarsa a kungiyar, damar da Pogba yake da ita ta ci gaba da zama a United ta karu - inda ake sa ran kasuwar musayar 'yan kwallon kafa za ta rushe saboda tasirin annobar Covid-19 kan harkokin kudin kungiyoyi.

Solskjaer ya ce: "Paul yana daya daga cikin kwararrun 'yan wasan tsakiya na duniya."

"Ya jagoranci lashe Kofin Duniya kuma ina son irin wannan shugabanci a filin wasa."

Pogba bai sake buga wa United wasa ba tun ranar 26 ga watan Disamba a yayin da yake kokarin komawa ganiyarsa bayan jinyar da ya yi, amma ya fuskanci koma-baya wanda ya sanya aka yi tiyata a kafarsa a watan Janairu.

A yayin da United za ta koma Gasar Firimiya a fafatawarda za ta yi da Tottenham ranar Juma'a - wata fiye da uku bayan an dakatar da gasar sanadin annobar korona - Solskjaer yana so dan wasan Faransa ya taka muhimmiyar rawa.

"Da yake yanzu ya komo kan ganiyarsa kuma zai iya buga wasa, na ga yadda lafiyarsa take, kuma a shirye yake ya sake murza leda," in ji Solskjaer.

"Ban sani ba ko zai yi miniti 45 ko 60 yana murza leda amma na san cewa a hankali zai warware, kuma muna fata nan da watanni kadan masu zuwa zai koma kamar yadda yake a baya."

BBC Sport ta fahimci cewa masu horaswa na United sun samu kwarin gwiwa yadda Pogba da Bruno Fernandes wanda aka dauko a watan Janairu suka shiga tawagar da ta buga wasan sada zumunci makon jiya inda West Brom ta doke ta a Old Trafford.