EFCC ta damke Godswill Akpabio

Mr Akpabio ya jagoranci Akwa Ibom tsawon shekaru takwas

Asalin hoton, BBC World Service

Bayanan hoto, Mr Akpabio ya jagoranci Akwa Ibom tsawon shekaru takwas

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Nigeria, EFCC ta damke Mr Godswill Akpabio, tsohon gwamnan jihar Akwa Ibom kuma shugaban marasa rinjaye a majalisar dattawan kasar.

Bayanai sun ce da yammacin ranar Juma'a ne jami'an EFCC din suka damke tsohon gwamnan.

Ana zarginsa ne da wawure dukiyar al'umma a zamanin mulkinsa a jihar ta Akwa Ibom.

Wata majiya a hukumar EFCC ta tabbatar da cewa ana yi wa Mr Akpabio tambayoyi a ofishin hukumar da ke Abuja.

Sai dai kuma wasu rahotanni na cewa tun a daren ranar Juma'ar ne hukumar ta saki mista Akpabion ya koma zuwa gidansa.

Mr Godswill Akpabio shi ne gwamnan jihar Akwa Ibom daga shekarar 2007 zuwa 2015.

A yanzu haka dai EFCC na binciken wasu daga cikin tsofaffin gwamnoni a Nigeria ciki har da Alhaji Sule Lamido na Jigawa da Murtala Nyako na Adamawa da Gabriel Suswan na Benue da kuma Ikedi Ohakim na jihar Imo.