Ambaliya ta yi barna a jihar Gombe

Rahotanni daga jihar Gombe da ke arewa maso gabashin Najeriya sun ce ambaliyar ruwa ta yi barna sosai a garuruwan Gombe da kuma Bajoga.
Rahotannin sun ce ambaliyar ruwan ta lalata daruruwan gidaje da gonaki, kuma al'amarin ya fi muni a garin Bajoga.
Lamarin ya faru ne sakamakon ruwan da aka tafka kamar da bakin kwarya a ranar Laraba.
A baya-bayan nan hukumomin Kamaru suka yi gargadin cewa za a iya samun ambaliyar ruwa a wasu sassa na Najeriya sakamakon bude madatsar ruwa na Lagdo.






