INEC ta ce Bamanga ne shugaban PDP

Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, ta tabbatar da Alhaji Bamanga Tukur a matsayin shugaban jam'iyyar PDP mai mulkin kasar.
Hakan na kunshe ne a wata wasika da hukumar ta aike wa shugaban PDP da ta balle Abubakar Baraje, bayan sun bukaci hukumar ta tabbatar da shi a matsayin shugaban PDP.
INEC ta ce ta sa ido a zaben jam'iyyar da aka yi a watan Maris na bara, wanda aka zabi Bamanga a matsayin shugaban jam'iyyar, saboda haka ba zai yiwu hukumar ta amince da wani ba.
Har ila yau a ranar Alhamin ne kuma, wata kotu a jihar Legas ta yi watsi da karar da bangaren Barajen ya shigar, na kalubalantar Bamanga Tukur, a bisa dalilin cewa ba ta da hurumin sauraron karar.







