Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 27/05/2025.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Aisha Babangida, Badamasi Abdulkadir Mukhtar da Zubairu Ahmad

  1. An ga watan Zulhijja a Najeriya

    Sarkin Musulmin Najeriya Muhammad Sa'ad Abubakar

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Sarkin Musulmin Najeriya Muhammad Sa'ad Abubakar

    Sarkin Musulmin Najeriya, Muhammad Sa'ad Abubakar ya ayyana Laraba, 28 ga watan Mayun 2025 a matsayin ɗaya ga watan Zulhijjan shekara ta 1446 bayan Hijira.

    Mai alfarman, wanda shi ne shugaban Majalisar ƙoli ta addinin Musulunci a Najeriya ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa, wadda ta samu sa hannun babban mashawarci ga sarkin Musulmin kan harkokin addini, Farfesa Sambo Wali Junaidu.

    Wannan sanarwa na nufin za a hau idin babbar sallah a Najeriyar a ranar Juma'a 10 ga watan na Zulhijja, wadda ta yi daidai da shida ga watan Yunin 2025.

    Hakan ya zo daidai da ganin watan ƙasar Saudiyya, wadda tun farko ta ayyana Laraba a matsayin ɗaya ga watan na Zulhijja, tare da cewa za a hau Arfa a ranar Alhamis, biyar ga watan Yuni.

    Zulhijja shi ne wata na 12 a kalandar Musulunci kuma an kwaɗaitar da Musulmai wajen yin ibadu a cikinsa domin samun albarka.

    A cikin watan ne kuma ɗimbin al'ummar Musulmi daga faɗin duniya ke taruwa a ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajji, wanda ɗaya ne daga cikin ginshiƙan addinin na Musulunci.

  2. An samu yamutsi wajen rabon kayan agaji a Gaza

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    An samu yamutsi a wajen bayar da agaji da ƙungiyoyi masu samun goyon bayan Amurka suka ƙaddamar a Gaza, kwana guda bayan ƙaddamar da shirin mai cike da ruɗani.

    Bidiyon da aka yaɗa ya nuna yadda dubban Falasɗinawa ture juna da wawason kayan agaji a cibiyar rabon kayan ƙungiyar Gaza Humanitarian Foundation's (GHF) a kudancin birnin Rafah.

    Ƙungiyar ta ce an kai wani lokaci da yawan mutanen da ke wajen suka fi ƙarfin jami'anta, saboda tsananin buƙata.

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce dakarunta sun yi harbi a sama domin gargaɗi.

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce bidiyon abinda ya faru a Rafah babban abin tashin hankali ne, kuma tana da tsari mai kyau na kai agaji ga mutanen yankin da yawan su ya zarce miliyan biyu.

  3. Jam'iyyar PDP ta kafa kwamitin shirya babban taronta na ƙasa

    ...

    Asalin hoton, pdp

    Jam’iyyar PDP ta kafa kwamitin da zai shirya babban taron jam’iyyar a ƙarƙashin gwamman Adamawa Amadu Fintiri.

    PDP ta ce majalisar zartarwar ta amince da kafa wani ƙarin kwamitin da zai yi nazari a kan tsarin karɓa karɓan muƙamai a jam'iyyar gabanin babban taronta, a ƙarƙashin Gwamnan jihar Bayelsa Douye Diri.

    Jamiyyar ta ɗauki wannan mataki ne a yayin zaman majalisar ƙoli da ta gudanar a ranar Talata a birnin Abuja.

    A yayin taron, jam'iyyar ta kuma yi Allah wadai da rufe hedikwatarta da hukumar kula da birnin Abuja ta yi, tare da shan alwashin bin kadin matakin.

    A ranar Litinin hukumar kula da birnin Abuja, FCTA ta garƙame hedikwatar PDP da aka fi sani da Wadata Plaza saboda rashin biyan harajin ƙasa, lamarin da ya janyo cece ku ce.

  4. An sanya hannu kan dokar lasisin rediyo a Zimbabwe

    Zimbabwe

    Asalin hoton, Bloomberg via Getty Images

    Shugaban Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, ya sanya hannu kan wata doka mai cike da cece-kuce da ta bukaci dukkan direbobi su biya wasu kudade a matsayin lasisin rediyon motocinsu.

    Wannan doka dai ta zo ne a daidai lokacin da wasu da dama ke kokawa kan matsalar tsadar rayuwa a kasar.

    Masu sukar lamarin na korafin cewa bai kamata su dauki alhakin tallafawa gidan rediyon gwamnati ba wanda su ke yi wa ganin kafa ce ta tallata jam'iyya mai mulki

    Matakin dai wani shiri ne na fadada hanyoyin samun kudaden shiga ga kafar yada labarai mallakar gwamnatin kasar amma masu sukar lamarin sun ce kudin lasisin ya yi yawa, musamman ganin halin da tattalin arzikin kasar ke ciki.

    A Zimbabwe ba za ka iya yin inshorar mota ba sai idan ka biya kusan dalar Amurka casa'in a shekara a matsayin kudin lasisin rediyo wanda zai shige aljihun gidan rediyon gwamnati.

    Akwai rahotannin mutane na tunanin cire rediyon motocinsu amma ko sun yi hakan ba za su tsira ba domin biyan kudin tilas ne ga duk wani wanda ya mallaki mota a kasar ko da kuwa ba ya sauraron gidan rediyon gwamnatin.

    Kalubalen da ke gaban gwamnati shi ne bullo da hanyoyin da za ta kara haraji yayin da mutane da yawa ke gudanar da al’amuransu a bangaren yan kasuwan da ba su cikin tsarin biyan haraji a hukumance .

    Da yake mayar da martani game da damuwar masu ababen hawa a shafukan sada zumunta, babban jami’i a ma’aikatar yada labarai ta kasar Zimbabwe Nick Mangwana, , ya ce sabuwar dokar ta zama dole kuma an bullo da ita ne saboda tabbatar da daidaito a al’umma.

  5. Sarki Charles ya kammala ziyarar Canada

    King Charles

    Asalin hoton, PA Media

    Sarki Charles da sarauniya Camilla sun kammala ziyarar da suka kai Canada.

    A yayin ziyarar Sarki Charles ya gabatar da jawabi cikin Turancin Birtaniya da kuma Faransanci a bikin ƙaddamar da majalisar dokokin Canada, inda ya ce a yau Canada na fuskantar wani lokaci mai muhimmanci.

    A cewar Sarki Charles, al'ummar Canada na fuskantar sauye-sauye da ba a taɓa gani ba a tarihin rayuwarsu.

    Ya ƙara da cewa alaƙar ƙasar da Amurka na sauyawa, inda ya jaddada ƴancin da duka ƙasashen biyu ke da shi.

    Firaiministan Canada, Mark Carney ya gayyaci Sarki Charles bayan nasarar lashe zaɓe da ya yi a baya-bayan nan.

    Karon farko ke nan da wani sarki ya gabatar da jawabi don ƙaddamar da majalisar dokoki cikin kusan shekara hamsin.

  6. Ƴan majalisar Faransa sun goyi bayan dokar taya mutum mutuwa

    France

    Asalin hoton, rikirennes/Getty Images

    Ƴan majalisar dokokin Faransa sun kaɗa ƙuri'ar goyon bayan dokar taya mutanen da suka kai gargara mutuwa a ƙasar.

    Majalisar wakilan ƙasar ta amince da ƙudirin dokar da ƙuri'a 305, yayin da aka samu ƴan majalisar 199 da suka kaɗa ƙuri'ar adawa da shi.

    Za a tafka muhawara kan ƙudirin a majalisar dattawa kafin amincewa da shi, kuma masu goyon baya na fatan a zartar da dokar zuwa shekarar 2027.

    Idan aka zartar da Ƙudirin dokar, Faransa za ta zama ƙasa ta takwas a cikin tarayyar Turai da ta amince da ita.

    A muhawarar da aka shafe makonni biyu aka tafkawa a majalisar dokokin Faransan, an yi tattaunawa mai tsawo a kan dalilan da za su kai har a amince da taimakawa marar lafiya ya mutu.

    Firaminista François Bayrou, wanda mabiyin ɗariƙar katolika ne ya ce da yana da damar kaɗa ƙuri'a zai janye ne, ya ƙi jefa ƙuri'ar.

  7. An ga watan Zhul Hijja a Saudiyya

    Wata

    Asalin hoton, Getty Images

    Mahukunta a Saudiyya sun sanar da ganin jinjirin watan Zhul Hijja.

    Sanarwar ta ce ranar Laraba 28 ga watan Mayu za ta zamo ɗaya ga watan Zhul Hijja, kuma hakan na nufin za a yi Arafah a ranar Alhamis 5 ga watan Yuni kuma a yi sallah a ranar Juma'a 6 ga watan Yunin.

  8. Ƙungiyoyin da Amurka ke goyon baya sun fara rabon agaji a Gaza

    GAZA

    Asalin hoton, AFP

    Wasu ƙungiyoyin agaji masu samun goyon bayan Amurka da Isra'ila sun fara aiki a Gaza.

    Ƙungiyar Gaza Humanitarian Foundation (GHF) ta ce manyan motoci ɗauke da abinci sun isa wuraren da ake da tabbacin tsaro, kuma an fara raba wa mutane.

    Ba ta dai bayyana wajen da aka kai kayan ba, ko kuma yadda aka shigar da su.

    Ƙungiyar tana aiki ne tare da jami'an tsaron Amurka da nufin kaucewa Najalisar Dinkin Duniya wadda ta ke kan gaba wajen raba agajai ga Falasɗinawa fiye da miliyan biyu a Gaza, yankin da ƙwararru suka yi gargaɗin faɗawa tarkon yunwa bayan da Isra'ila ta hana shigar da agaji tsawon makonni 11..

    Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji da dama sun ƙi amincewa da tsarin ƙungiyar GHF saboda matsayar su cewa sun saɓawa tsarin bayar da agaji na duniya wanda ya hana a shigar da sojoji wajen rabon.

  9. Manyan hafsoshin tsaron Afirka na ganawa a Moscow

    Manyan hafsoshin tsaro daga sassan ƙasashen Afirka na ganawa a Moscow a daidai lokacin da Rasha ke neman ƙarfafa tasirinta a nahiyar.

    Daga cikin mutanen da ke halartar taron akwai ministoci daga Nijar da Burkina faso da Mali - ƙasashen da a yanzu ke ƙarƙashin mulkin soji.

    Ƙasashen uku kuma sun fice daga ƙungiyar raya tattalin ƙsashen yammacin firka ECOWAS kuma sun nesanta kansu daga ƙasashen Yamma inda suka kafa ƙungiyar AES.

    Ƴanjarida sun ce ƙasashen Afirka da dama za su nemi faɗaɗa alaƙarsu ta tsaro sannan za su so taimakon Rasha wajen magance matsalolin ƙungiyoyi masu iƙirarin Jihadi.

  10. Ana fargabar ɓarkewar annoba a Sudan

    Sudan

    Asalin hoton, Kevin McGregor / BBC

    Ƙungiyoyin agaji a Sudan sun yi gargaɗin yiwuwar faɗa wa bala'in da zai shafi lafiyar al'umma yayin da cutar amai da gudawa da sauran cututtuka masu saurin kisa ke bazuwa daidai lokacin da kuma ɓangaren lafiya a ƙasar ke fama da ƙalubale.

    Kusan mutum 350 ne suka mutu a makonnin baya-bayan nan sakamakon cutar ta kwalara a Khartoum, babban birnin ƙasar.

    Ƙungiyoyin agaji sun ce lamarin na faruwa ne sakamakon shekaru biyun da aka shafe ana yaƙi ba ƙaƙƙautawa.

    Hare-haren jirage mara matuƙa kan cibiyoyin lantarki a birnin Omdurman sun tilasta wa mutane shan gurɓataccen ruwa.

    An lalata asibitoci da dama a Sudan inda ƙungiyar agaji ta MSF ta ce asibitoci ƙalilan da suka rage sun cika maƙil da marasa lafiya.

  11. Netanyahu na fuskantar matsin lamba kan jinkirin ceto Isra'ilawan da Hamas ta kama

    Benjamin Netanyahu

    Asalin hoton, Getty Images

    Iyalan mutanen da ƙungiyar Hamas ke tsare da su sun caccaki Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu saboda yadda ake ƙwallafa masu ran sakin ƴan'uwansu amma suka ji shiru.

    A wani saƙon bidiyo da ya yi ranar Lahadi, Mista Netanyahu ya ce a cikin ƴan kwanaki masu zuwa, yana fatan sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da kuma sakin mutanen da ke hannu.

    Sai dai ofishinsa ya janye kalaman Firaiminsitan. Ɗan'uwan ɗaya daga cikin waɗanda ake garkuwa da su ya zargi Mista Netanyahu da sanya tsoro a zukatansu.

  12. Tinubu ya nemi amincewar majalisa domin ciyo bashin dala biliyan 21.5

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/Facebook

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya aike wa majalisar dattawa da buƙata inda yake neman izini domin karɓo bashin dala biliyan 21.5 daga ƙasashen waje da kuma naira biliyan 758 daga cikin gida.

    Ana sa ran za a yi amfani da kuɗin wajen aiwatar da muhimman ayyuka kamar gyaran hanyoyi da kiwon lafiya da ilimi da samar da ruwan sha da kuma biyan tsoffin ma’aikata haƙƙoƙin fansho da ake bin su a ƙarƙashin tsarin Fansho na Gwamnati

    Majalisar ta tura buƙatar zuwa kwamitinta mai kula da lamurran bashi na cikin gida da na waje, wanda ake sa ran zai kawo rahoto cikin makonni biyu.

    Haka kuma, Shugaban ya buƙaci a ba shi damar cin bashin ƙarin dala biliyan biyu daga kasuwar cikin gida domin saka jari a wasu sassa masu muhimmanci na tattalin arziƙi wanda shi ma majalisar za ta tura zuwa ga kwamitin basussuka na gida da waje domin nazari.

    A baya, Tinubu ya rubuta wa majalisar yana neman amincewa da sabon shirin rancen kuɗi na shekarar 2025 zuwa 2026.

  13. Ghana ta rufe ofishin jakadancinta da ke Washington DC

    ...

    Asalin hoton, Embassy of Ghana, Washington DC

    Ƙasar Ghana ta rufe ofishin jakadancinta da ke Washington DC na Amurka na ɗan lokaci saboda bincike kan badakalar biza.

    Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa ne ya sanar da hakan, yana mai cewa an rufe ofishin ne saboda ana gudanar da bincike kan ma'aikatan ofishin waɗanda ake zargi da aikata abubuwan da suka karya doka.

    Dukkan ma’aikatan diflomasiyyar an janye su zuwa gida, yayin da ma’aikatan da aka ɗauka a cikin ƙasar Amurka su ma an dakatar da su daga aiki.

    Binciken ya gano wasu ayyuka na cin hanci ciki har da wani ma’aikacin fasaha da aka ɗauka cikin gida wanda ake zargin ya ƙirƙiri wata hanyar bogi a shafin intanet na ofishin wanda ke tura masu neman biza da fasfo zuwa wani kamfani mai zaman kansa mai suna Ghana Travel Consultants (GTC), da ke cajin kuɗaɗen da suka kama daga dala 29.75 zuwa dala 60, ba tare da samun izini daga ofishin ba.

  14. Shugaban gwamnatin sojin Nijar ya sauke gwamnan jihar Tahoua

    ...

    Asalin hoton, AFP

    Shugaban majalisar mulkin sojojin Jamhuriyar Nijar, Janar Abdourahamane Tchiani ya sauke gwamnan jihar Tahoua, Kanal Oumarou tawaye tare da maye goubinsa cikin gaggawa da Kanal Souleymane Amadou Moussa.

    Hakan dai na zuwa ne kwanaki biyu bayan da sojojin ƙasar aƙalla 49 suka rasa rayukansu yayin wani hari da ƙungiyar IS ta ɗauki alhakin kaiwa a a garin Eknewan da ke yankin Tillia na jihar Tahoua, da ta yi iyaka da ƙasar Mali. Har yanzu dai gwamnatin kasar bata ce uffan ba game da wannan hari, majiyar kusa da tsaron kasar na cewa yan bindigar da ke saman babura su fiye da 200.

    Haka ma bayanai sun ce maharan sun yi amfani da jirage marasa maƙuka wajen tarwatsa sansanin.

  15. Sojoji sun daƙile harin Boko Haram a garin Marte da ke Borno

    ...

    Asalin hoton, Defence HQ/X

    Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation Hadin Kai sun yi nasarar daƙile wani hari da ‘yan Boko Hara da /ISWAP suka kai da tsakar dare a garin Marte ta Jihar Borno.

    Harin wanda ya fara da misalin karfe 1:35 na daren ranar Litinin, ya janyo arangama mai zafi tsakanin sojojin Najeriya da ƴan Boko Haram ɗin inda sojojin suka kashe da dama daga cikin su.

    Rundunar sojin ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X.

    Rundunar ta kuma tabbatar da mutuwar sojoji biyu a yayin faɗan, yayin da sojojin suka ci gaba da bin sahun masu ƴan Boko Haram ɗin da suka tsere.

    Garin Marte dai na daga cikin wuraren da Boko Haram ke yawan kai hari saboda matsayinsa na tasha da hanyar shiga garuruwa

    Gwamnan Jihar, Babagana Umara Zulum, ya taba yin kira ga gwamnatin tarayya da ta ƙara azama wajen ƙarfafa ayyukan tsaro a garin Marte da kuma kare garin da komawa hannu ƴan Boko Haram.

    Harin da aka kai na ranar Litinin ya sake tunatar da yadda Boko Haram ke ci gaba da zama barazana ga ƴan Najeriya.

  16. Cin zalin yara ba shi da gurbi a Najeriya - Tinubu

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cin zalin yara a matsayin abin Allah-wadai da ya ce ba za a lamunta da ci gaba da shi ba a Najeriya.

    Tinubu ya sanar da hakan a cikin wani bayani da aka fitar a yau Talata albarkacin Ranar Yara ta ta duniya bana.

    "Al'ummar da yara ke samun kulawa da natsuwa, ake martaba su tare da sauraren su a sarari da kuma sauran ɓangarori a cikin, ita ce mai samun cigaba a duniya. A zahiri ya ke cin fuskar yara da walaƙanta su ba shi da muhalli a Najeriya," in ji shugaba Tinubu.

    Shugaban Najeriyar ya ce ƙasarsa na cikin na gaba-gaba da ake cin zarafin yara a makarantu da sauran wurare, "A duniya, yaro ɗaya a cikin uku na fuskantar cin zali. Bincike ya nuna a Najeriya yawan samun cin zalin yara 'yan shekarun zuwa makaranta ya kai kashi 65 cikin ɗari, waɗanda ke fuskantar hakan a zahiri da kuma ke da illa ga tunani ko alaƙarsu da sauran jama'a. Duk yaron da ke koyo cikin halin tsoro ba zai taɓa gane kome ba,” in ji Tinubu.

    Shugaban Najeriyar ya ce gwamnatin tarayyar ƙasar da jahohi na ɗaukar matakan da suka dace domin kare yara daga fuskantar cin zarafi, waɗanda ya bayyana da "manyan gobe kuma ƙashin bayan ci gaban ƙasa".

  17. Falalar goman farko ta Zhul Hajji tare da Sheikh Imam Junaidu Abubakar

    Bayanan bidiyo, Latsa alamar da ke sama domin kallo

    Matashin malami a Najeriya, Sheikh Junaid Abubakar ya lissafa wasu ayyuka da ya kamata Musulmi su yi a ranakun goman farkon watan Dhul Hajji wata na 12 a jerin watannin Musulunci.

    Shehun malamin ya ce kwanakin 10 na watan sun ƙunshi ibadu kamar azumi da salloli da zikiri da karatun al'ƙur'ani da kuma layya ga masu hali.

    Ya kuma ƙara da cewa babbar rana a kwanakin ita ce ranar tara ga wata wato ranar Arfa.

  18. Gwamnati ta ba masu filaye a Abuja wa'adin biyan haraji ko a ƙwace

    ...

    Asalin hoton, Wike/X

    Gwamnatin Najeriyar ta bayar da wa'adin ne na kwana 14 rak ga masu filaye da gidajen da ke birnin tarayyar da yawansu ya kai 4,794 waɗanda suka yi biris da ƙin biyan haraji ga filayen.

    Ministan babban birnin tarayyar Najeriya Nyesom Ezenwo Wike, ya ce sabon tsarin zai shafi masu filaye da gidaje da kezaune tsakiyar Abuja da aka nemi su biya naira miliyan 5 tare da sauran kuɗaɗen da ake bin su bashi a baya. Sai masu kadarorin a Maitama da Asokoro da Wuse II da Guzape, su kuma za su biya harajin naira miliyan 3, yayin da masu filayen da ke Wuse I da Garki I da Garki II an dora mu su biyan naira miliyan 2.

    Ministan ya ce wannan mataki ne da gwamnatin ƙasar ta fito da shi domin tabbatar da masu filaye sun kiyaye dokokin biyan haraji da kuma tafiyar da su yadda ya dace.

    Haka ma ministan birnin tarayyar Najeriyar ya ce za su ɗauki matakin ladaftar da waɗanda suka mallaki gidaje da sauran kadarorin da ba su yi musu rajista ba, inda su ma aka ba su wa'adin kwana 14 da su yi wa filayen da sauran kadarorin rajista kafin cikar wa'adin ko su fuskanci ƙwacewa.

    Mista Wike ya ce matakan da gwamnatin tarayya na buƙatar a tabbatar da an biya harajin dukan gidaje da filaye akan lokaci kasancewar abu ne mai muhimmanci a ɓangaren bunƙasa birnin na Abuja tare da samar da aikin yi ga jama'a.

  19. Kenya ta yi watsi da sukar da Amurka ta yi mata kan China

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Majalisar Dokokin Kenya ta yi watsi da sukar da Majalisar dokokin Amurka ta yi mata akan alaƙarta da ƙasar Sin, wanda ke nufin tana ci gaba da ja baya daga dangantakarta da Washington.

    Shugaban kwamtin tsaro da harhohin ƙasashen waje na Kenya Nelson Koech dai ya ce ƙasarsa na da cikakken 'yancin yin hulɗa da kowace ƙasa a duniya a ɓangarori da dama musamman na tallin arziki.

    "Kenya na neman haɗaka da sassan duniya, daga ciki Afirka na bayar da gagarumar gudummuwa ga ɓangarorin da suka shafi ci gaban duniya da tattalin arziki. Wannan ya nuna manufar gwamnatin shugaba Trump na fiito da sabbin tsare-tsare da suka shafi cibiyoyi da ƙasashen duniya," in ji Nelson Koech.

    Wannan sabuwar jayayyar dai ta soma ne bayan da shugaban kwamtin hulɗa da ƙasashen waje na majalisar dokokin Amurka, Jim Risch ya gargaɗi Kenya akan abin da ya kira alaƙa mai "illa" tsakanin ta da China, bayan da shugaban ƙasar Kenya William Ruto ya goyi baya tare da neman a samar da gamayya ɗaya da za ta haɗa kan duniya wadda kuma China za ta jagoracin samar da ita.

    Ruto ya bayyana hakan ne a wata ziyara da ya kai China a watan Afirilu.

  20. Ɓarkewar cutar kwalara ta hallaka dubban mutane a Khartoum ta Sudan

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Aƙalla mutane 346 ne suka rasa rayukansu sakamakon ɓarkewar cutar kwalera a jihar Khartoum da ke Sudan, tare da ɗaruruwan wasu da suka kamu da cutar yayin da annobar ke ci gaba da yaɗuwa a yankin, kamar yadda gidan jaridar Sudan Tribune ya ruwaito.

    Shugaban ma'aikatar lafiya a jihar, Fath Al-Rahman Al-Amin, ya bayyana cewa ana samun sama da sabbin mutane 80 da ke kamuwa da cutar kullum, kuma ya sanar da kafa cibiyoyin killace marasa lafiya guda 15 domin daƙile yaɗuwar cutar.

    A ranar 14 ga Mayu, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa ta miƙa kaya masu nauyin tan 15 na kayan lafiya ga ma’aikatar lafiya a Khartoum domin tallafa wa ƙoƙarin daƙile annobar.

    Ma’aikatar Lafiya ta ƙasa ta Sudan ta ce za ta ƙaddamar da kamfen ɗin rigakafin kwalera a Khartoum domin rage yaɗuwar cutar.

    Rahotannin kafafen yaɗa labarai na cikin gida sun danganta barkewar cutar da amfani da ruwa daga wuraren da ba su da tsafta da kuma rashin tsafta.