Abin da ya sa na koma APC - Gwamnan Zamfara
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma shari’o’in da suka dabaibaye tsohuwar jam'iyyarsa ta PDP ne babban dalilan da suka sa ya fice daga jam'iyyar zuwa APC.
A ranar Litinin ne gwamnan ya sanar da sauya sheƙarsa daga PDP zuwa jam'iyya mai mulki ta APC a hukumance bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.
A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa ficewar gwamnan zuwa APC ya zama dole saboda muradun al’ummar Zamfara.
Sanarwar ta ce gwamnan ya ɗauki matakin komawa APC ne bayan shawarar masu ruwa da tsaki a jihar, musamman duba da matsalolin shari’a da jam'iyyar PDP ke fuskanta a halin yanzu.
Gwamna Dauda Lawal ya ce ya yi baƙin ƙoƙarinsa don ganin ya sasanta rikicin da ke tsakanin ɓangarorin jam’iyyar domin tabbatar da haɗin kai da kuma damar tsayar da ƴan takara a zaɓuka masu zuwa.
“Amma ƙoƙarin samar da zaman lafiya da sasanci ta hanyar sulhu bai yi nasara ba, lamarin da ya haifar da jerin shari’o’i da ka iya yin tasiri ga ‘yan siyasar da za su nemi takara a zaɓen shekarar 2027.” in ji sanarwar.
Ficewar Dauda Lawan daga PDP na zuwa ne mako guda byan ficewar gwamnan Adamawa daga PDP zuwa APC, inda a yanzu jam'iyyar na da gwamnoni 2 kacal, inda APC ke da 31.