An kaddamar da jirgin kasa mafi gudu a Nigeria

Shugaba Buhari ne ya kaddamar da sabon jirgin
Bayanan hoto, Shugaba Buhari ne ya kaddamar da sabon jirgin

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya kaddamar da sabon jirgin kasa na fasinja wanda zai dinga zirga-zirga tsakanin Abuja zuwa Kaduna a wani kasaitaccen biki a ranar Talata.

A yayin bikin kaddamarwar, shugaban ya yi tafiyar minti 18 a jirgin daga tashar Idu zuwa ta Kubwa tare da dumbin jama'a.

  • <link type="page"><caption> Hotunan kaddamar da jirgin kasa mafi gudu a Nigeria</caption><url href="http://www.bbc.com/hausa/multimedia/2016/07/160726_picgallery_nigeria_launches_speed_train.shtml" platform="highweb"/></link>Za mu kawo muku karin bayani nan ba da jimawa ba.

Daga nan sai jirgin ya wuce birnin Kaduna a tafiyar kilomita 120 zuwa 150 a duk sa'a daya.

Za a dinga cajin fasinjojin jirgin naira 500 daga Abuja zuwa Kaduna.

Jirgin shi ne irinsa na farko mafi gudu da aka kaddamar a Najeriya, kuma yana yin tafiyar sa'o'i biyu ne tsakanin Abuja da Kaduna.

An bayar da aikin kwangilar jirgin ne tun zamanin mulkin shugaban Cif Olusegun Obasanjo, amma sai a lokacin shugaba Jonathan aka kadaamar da aikin, duk da cewa bai fara aiki a lokacin ba sai a yanzu.

Wannan dalili ne yasa jam'iyyar adawa ta PDP wadda ita ce ta tsohon shugaba Jonathan din take ta wallafawa a shafinta na Twitter cewa a karkashin mulkinta ne aka yi wannan ''hobbasa''.

Ta kuma ce shugaba Buhari ya samu damar kaddamarwar ne kawai amma ba ''kokarinsa'' ba ne.