Faransa ta ce ta kashe jagoran al-Qaeda a arewacin Afirka

Asalin hoton, AFP
Faransa ta ce ta kashe jagoran ƙungiyar al-Qaeda na arewacin Afirka, Abdelmalek Droukdel, a wani samame cikin ƙasar Mali.
Ministar tsaron ƙasar Florence Parly ta ce an kashe Droukdel tare da wasu na hannun damansa ranar Laraba a arewacin ƙasar.
Ta kuma ce dakarun Faransa sun kama wani babban kwamandan ƙungiyar IS yayin wani aikin soji cikin watan Mayu a Mali.
A cewarta samamen na hatsabibanci sun yi mummunar illa ga ƙungiyoyin 'yan ta'addan.
"Dakarunmu, da haɗin gwiwar abokan ƙawancensu a Sahel, za su ci gaba da farautar su ba ji ba gani," in ji ministar.
A matsayinsa na shugaban Al-Qaeda a Maghreb wato (AQIM), Droukdel shi ne jagoran duk rassan ƙungiyar a arewacin Afirka kuma yana jagorantar reshen al-Qaeda a yankin Sahel, wato Jamaat Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM).
Shi kuma kwamandan ƙungiyar IS da aka kama, Mohamed Mrabat, tsohon mayaƙi ne na masu iƙirarin jihadi kuma ya riƙe babban muƙami a reshen ƙungiyar mai suna Islamic State in the Greater Sahara (ISGS), in ji Misis Florence Parly.
Ta ce an kama shi ne ranar 19 ga watan Mayu.
A ranar 7 ga watan Mayu ne ƙungiyar IS ta bayyana cewa mayaƙanata sun gwabza wani ƙazamin faɗa da takwarorinsu na ƙungiyar Al-Qaeda a Mali da Burkina Faso.
Ta kuma zargi mayaƙan ƙungiyar Jamaat Nusrat al-islam wal-muslimin JNIM da kai hare-hare kan tungoginta tare da datse hanyar da take samun man fetur da kuma tsare magoya bayanta.











