Aisha Buhari: 'Matsalar fyade na tayar mini da hankali'

Aisha Buhari

Asalin hoton, Twitter/@aishambuhari

Lokacin karatu: Minti 1

Aisha Buhari, mai dakin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ta ce labarin da take samu game da yawaitar yi wa mata fyade yana matukar tayar mata da hankali.

A sakon da ta wallafa ranar Laraba a shafinta na Twitter, Aisha Buhari ta ce: "Abin tayar da hankali ne samun labarin kisan da ake yi wa 'ya'yanmu mata, wadanda maza suke yi wa fyade na rashin imani; wasu lokutan ma iyayensu da 'yan uwansu da kuma masu kula da su ne suke yin hakan."

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Matsalar fyade dai tana neman zama ruwan dare a Najeriya, inda a baya bayan nan aka samun labarin yi wa wasu mata fyade a sassa daban-daban na kasar.

Daya daga cikinsu ita ce wata yarinya mai shekara 12 wacce ta shaida wa 'yan sanda a jihar Jigawa da ke arewa maso yammacin kasar cewa wasu mutum 12 sun shafe wata biyu suna yi mata fyade.

Kazalika, a makon jiya an zargi wasu mutane da kisan wata ɗaliba ƴar jami'a bayan sun yi mata fyade a jihar Edo da ke kudancin Najeriya.

Masu rajin kare hakkin yara a Najeriya na ganin cewa za a ci gaba da fuskantar matsalar fyade ga kananan yara a kasar matukar gwamnati ba ta fara aiwatar da hukuncin kisa a kan masu aikata irin wannan laifi ba.