Rashin Tsaro: Sojojin Nigeria sun kashe 'yan fashi 27 a Zamfara

Dakarun sojojin Najeriya

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, A baya-bayan nan sojojin Najeriya bayyana nasarorin da take samu kan 'yan bindiga amma babu kafa mai zaman kanta da ke tabbatar da rahotannin
Lokacin karatu: Minti 1

Hedikwatar rundunar sojojin Najeriya da ke Abuja, babban birnin ƙasar ta ce ta halaka 'yan fashi 27 a kan iyakar jihohin Zamfara da Katsina.

A samamen da rundunar tsaro ta musamman mai laƙabin Hadarin Daji ta kai wa 'yan fashin ranar Alhamis, an kashe su tare da lalata wasu daga cikin sansanoninsu bayan samun wasu bayanan sirri, kamar yadda rundunar ta bayyana a wata sanarwa a shafinta na Twitter.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Rundunar ta ƙara da cewa bayan samun rahotannin sirrin ne kuma ta bazama, inda jiragenta mai saukar ungulu da kuma mai kai hari ta sama suka isa matsuguninsu da ke haɗakar garuruwan Nahuta da kuma Doumborou.

A baya-bayan nan sojoji na bayyana irin nasarar da suke samu a kan masu ɗauke da makamai, sai dai babu wata kafa mai zaman kanta da ke tabbatar da nasarorin.

Gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhamnmadu ta ce tana bakin ƙoƙarinta amma ko a ranar 20 ga watan Afirlu an samu rahoton mutum 47 da 'yan bindiga suka kashe a Katsina.

Yankin jihohin Zamfara da Katsina da Sokoto suna fama da hare-haren 'yan fashi a baya-bayan nan kuma hakan ya haddasa rasa rayuka da dama tare da raba wasu da mahallansu.