Najeriya ta tabbatar da bullar Coronavirus a Lagos

Cutar Corononavirus

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Najeriya ta shiga jerin kasashe 48 da cutar coronavirus ta bulla
Lokacin karatu: Minti 2

Hukumomi a Najeriya sun tabbatar da bullar cutar coronavirus da ake kira Covid-19 a jihar Lagos.

Ma'aikatar lafiya ce ta tabbatar da bullar cutar a sanarwar da ta wallafa a Twitter, inda ta ce a karon farko an samu bullar cutar a Najeriya tun barkewarta a China a watan Janairun 2020.

Kauce wa X, 1
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 1

Haka ma cibiyar da ke yaki da cututuka masu yaduwa a Najeriya ta wallafa a Twitter inda ta ce ministan lafiya ya tabbatar da bullar cutar a jihar Lagos.

Kauce wa X, 2
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X, 2

A sanarwar da ya fitar, ministan lafiya na Najeriya Dr Osagie Ehanire ya ce wani dan Italiya ne da ke aiki a kasar ya shigo da cutar bayan ya dawo daga Milan zuwa Lagos.

"Sakamakon gwaji da aka gudanar a asibitin koyarwa na jami'ar Lagos ya tabbatar da yana dauke da cutar."

"Ana duba lafiyarsa a asibitin kula da cutuka masu yaduwa a Yaba, kuma marar lafiyar bai nuna alamomi masu muni ba," in ji shi.

Ya kuma ce gwamnati ta kara tsaurara matakai domin tabbatar da dakile yaduwar cutar.

Tun a ranar Laraba ne ake ta yada jita-jitar labarin bullar cutar a Lagos a shafukan intanet bayan kwantar da wani dan China a asibitin Reddington da ke Ikeja.

Daga baya asibitin ya karyata labarin amma bai musanta zuwan dan China ba a asibitin domin diba lafiyarsa da ake fargabar yana dauke da cutar mai yin kisa a China.

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce cutar coronavirus ta kai wani matsayi na zama annoba a duniya saboda yadda take yaduwa.

Najeriya yanzu ta shiga jerin kasashen duniya da aka samu bullar cutar ta da ake kira COVID-19, kasa ta uku da aka samu bullarta a Afirka bayan Masar da Aljeriya.