A rika biyan marasa aiki albashi a Najeriya – Sanatoci

Asalin hoton, Getty Images
Majalisar Dattawa a Najeriya ta bukaci gwamnatin kasar ta dauki matakan gaggawa a kan matsalar rashin yi aiki a tsakanin 'yan kasar.
A mahawararsu a kan kudurin da Ike Ekweremadu ya gabatar kan matsalar rashin aikin yi a yau Laraba, sanatocin sun ce gazawar gwamnati wurin samar wa 'yan kasa ayyuka na da matukar hadari.
'Yan Majalisar na kuma neman gwamantin ta kafa asusun tallafa wa 'yan kasar marasa aiki zuwa lokacin da za su samu aikin yi.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Sun kara da cewa da yawa daga cikin matasan kasar da suka kammala karatu ba su da aiki.
Majalisar ta bukaci dukkan matakan gwamantin kasar su sanya dokar ta-baci a kan rashin aiki yi tsakanin al'umma, musamman matasa. Sannan a bude shirin samar da ayyukan yi ga matasa karkashin ma'aikatar tsare-tsare ta kasa.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Bayan haka ya kamata gwamanti ta bai wa kamfanonin 'yan kasuwa damar yin aiki ba tare da matsi ba, ta yadda za su iya daukar matasa aiki, kamar yadda sanatocin suka yi kira.







