Abba Kyari da Boss Mustapha: Buhari ya sake nada su a karo na biyu

Asalin hoton, Nigeria Presidency
Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya sake nada Abba Kyari a matsayin shugaban ma'aikata na fadarsa da kuma Boss Gida Mustapha a matsayin babban sakataren gwamnatin tarayya.
Mai bai wa shugaban shawara kan kafafen yada labarai Bashir Ahmad ne ya sanar da hakan a shafinsa na Twitter a ranar Juma'a.
Ya ce nadin nasu zai fara aiki ne daga ranar 29 ga watan Mayun 2019, wato ranar da shugaban ya sha rantsuwar karbar mulki a karo na biyu.
Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da wasu 'yan Najeriya ciki har da 'yan jam'iyyar APC ke nuna adawa da ci gaba da kasancewar Abba Kyari a matsayin shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasar.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Waiwaye
A farkon makon da ya gabata ne 'yan Najeriya suka sako gwamnatin Shugaba Buhari a gaba a shafukan sada zumunta tare da kiraye-kirayen a kori wasu na gaba-gaba a gwamnatinsa.
Mutane da dama ne suka yi ta bayyana ra'ayoyinsu a Twitter, inda suke kiran da a kori Abba Kyari shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa daga mukaminsa da kuma Mamman Daura.
Mamman Daura dan uwa ne na kusa ga shugaban - Buhari baffansa ne - kuma duk da cewa ba shi da mukami a gwamnatin amma ana hasashen cewa yana da fada-a-ji a fadar ta shugaban kasa.
Wannan ya biyo bayan wata zanga-zangar da wasu matasan jam'iyyar APC mai mulki suka yi ne a ranar Litinin domin neman shugaban da ka da ya sake nada ministocin da suka ce sun "hana ruwa gudu a wa'adinsa na farko".
Sannan kuma sun yi zargin cewa ministocin "ba sa son talaka, kuma ba su da gaskiya."
A wancan lokacin wasu sannanun mutane ma irin sy Sanata Shehu Sani ba a bar su a baya ba, inda ya tofa albarkacin bakinsa a Twitter yana cewa:
"Wannan zanga-zanga ana yi ne tsakanin 'yan tsirari masu fada-a-ji na fadar shugaban kasa da kuma gungun matasa domin neman iko a fadar gwamnati."
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Wasu da dama sun saka hotunansu a wurin zanga-zangar da suka yi ta ranar Litinin suna yin zambo da ba'a da sauran kalamai iri-iri kan Abba Kyari da Shugaba Buhari da Mamman Daura.
@lifeinarewa ya ce '"Yan Najeriya ba Abba Kyari suka zaba ba, ba kuma Mamman Daura ba."
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 3
@OlayinkaLere ko cewa ya yi: "Ko da Buhari ya kai miliyan daya (saboda karfin isar mulkinsa) ba zai taba korar Abba Kyari ba."
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 4
@PaulPositive4 shagube yake yi cewa wasu suna tunanin Buhari zai kori Abba Kyari, ta yaya Buhari zai kori kansa?
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 5
Ammai mai magana da yawun shugaban, Malam Garba Shehu, ya gaya wa BBC cewa wasu masu neman mukami ne suka debo mutane domin yin zanga-zangar.
"Wasu sun sa ido kan wadannan mukamai saboda wasu bukatu nasu," in ji shi.











