Amurka ta bude ofishin jakadancin ta a Somaliya

Ana cigaba da samun sauki a fannin tsaro a Mogadishu duk da qungiyar Al-Shabab tana cigaba da zama barazana

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Ana ci gaba da samun sauki a fannin tsaro a Mogadishu duk da kungiyar Al-Shabab na ci gaba da zama barazana

Kasar Amurka ta sake bude offishin jakadancinta a Somaliya bayan ofishin ya shafe kusan shakara 30 a rufe.

Amurkar ta bayyana cewa wannan abun tarihin yana bayyana irin cigaban da kasashen Afirka ta gabas suke samu.

Amurka ta kulle ofishin jakancinta a Somaliya a shekarar 1991 a lokacin da ake tsakiyar yaki tsakanin 'yan tawaye da gwamnati.

Hakan ya yi sanadiyar Amurka ta janye Jakadanta da Ma'aikatanta a kasar.

Shugaban Amurka Donald Trump ya kara fadada yakin da ake yi da kungiyar Al-Shabab a shekarar 2017, inda dakarun Amurka suka kai hare-hare sama da 24, wanda hakan ya hada da amfani da jirgi mara matuki domin kai hare-haren a wannan shekarar.

Tarihi ya nuna cewa, shugabanin kasar Amurka na baya suna kauce wa tsoma bakinsu a rikicin Somaliya tun bayan kashe dakaru na musamman na Amurka guda 18 da aka yi a Mogadishu a shekarar 1993, wanda aka yin Fim mai taken "Black Hawk Dawn" a kan wannan yaki na Somaliya.