An kara sanya dokar hana zirga-zirga a Kaduna

Gwamnna Kaduna Nasir El-Rufai

Asalin hoton, Twitter / @GovKaduna

Bayanan hoto, A ranar Talata ne Gwana Nasir El-Rufai ya jagoranci taron majalisar tsaro ta jihar
Lokacin karatu: Minti 1

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sake sanya dokar hana zirga-zirga ta sa'o'i 24 a garin Kaduna da kewaye a ranar Juma'a.

Gwamnan jihar Nasir el-Rufa'i ne ya bayyana hakan ta shafinsa na Twitter.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Hakazalika ya ce dokar ta shafi garin Kasuwan Magani da Kajuru da Katari da kuma Kachia, kuma ta fara aiki ne daga karfe 11 na safiyar Juma'a.

Gwamnan ya ce an dauki matakin ne bayan kashe wani basarake HRH Agom Adara a ranar Juma'a wanda aka sace a makon jiya.

Daga nan ya bukaci al'ummar jihar da su kwantar da hankulansu,inda ya ba da tabbacin hukunta wadanda suka aikata hakan.

A ranar Laraba ne aka sassauta dokar hana zirga-zirga ta sa'o'i 24 a garin Kaduna zuwa sa'o'i 13.

A ranar Litinin da dare ne gwaman ya sanar da mutanen jihar cewa mutum biyar ne suka rasa rayukansu a rikicin na baya-bayan nan a yayin wani jawabi da ya yi ta kafofin yada labarai.

Amma akwai rahotannin da ke cewa wadanda suka mutu sun kai mutum 26.

Hakazalika ya ce an kama mutane da adama da ake zargi da hannu wajen tayar da rikicin.

Ya kuma ce za a hukunta dukkan wadanda aka samu da laifin tayar da wannan hatsaniyar.