Sanatoci nawa ne ke goyon bayan Buhari, an yi 'ruwan kudi' a bikin 'yar Dangote

An bai wa Buhari lambar yabo ta 'boge'

Cibiyar The King Center, wacce ke adana tarihin fitaccen bakar fatar nan na Amurka, marigayi Martin Luther, ta nesanta kanta daga lambar yabon da aka bai wa Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya.

An kashe fiye da mutum 60 a Zamfara

Mazauna wani kauye da ke jihar Zamfara a arewacin Najeriya sun ce barayin shanu sun kashe sama da mutum 60 a kwanaki biyu da suka wuce.

An hana El-Rufai karbar bashin naira biliyan 126

Majalisar dattawan Najeriya ta yi watsi da bukatar da gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya gabatar mata ta cin bashin $350m (naira biliyan 126) daga Bankin Duniya.

'Yan majalisarsun yi watsi da bukatar karbo bashin ne "saboda Kaduna ita ce jiha ta biyu da ta fi yawan bashin da ake bin ta".

Karanta karin wasu labaran

Kalli bidiyonmu na yau

Domin samun karin bayani da kuma tofa albarkacin bakinku a kan wadannan labaran, sai ku garzaya shafinmu na BBC Hausa Facebook.