Taron addu'o'in jagoran 'yan adawa a Zimbabwe

Asalin hoton, Reuters
Shugaban kasar Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa, ya mika ta'aziyyarsa bisa ga rashin da aka yi na jagoran 'yan adawa, Morgan Changirai, wanda ya mutu sakamakon cutar kansa a makon da ya gabata.
Mr Mnangagwa, ya bayyana marigayin a matsayin wani muhimmi a siyasar kasar wanda kuma ya dace a rinka tunawa dashi a tarihin kasar.
Daga nan ya yi kira ga al'ummar kasar da su hadu domin nuna alhininsu ga babban rashin da aka yi.
Taron aduu'oin da aka yi a wani coci da ke Harare, ya samu halartar daruruwan mutane daga sassan kasar.
Kazalika daruruwan magoya bayan 'yan adawar kasar sun taru a wajen cocin, sanye da jajayen kaya, launin jam'iyyarsu.
A ranar 15 ga watan Fabrairu ne Allah ya yi wa Tsvangirai rasuwa yana da shekara 65 a duniya.
A ranar Talata ne za a binne gawarsa a kauyensa da ke Buhera.







