Mutum uku ne suka kamu da cutar kyandar biri a Nigeria – WHO

Kimanin shakaru 40 ke nan rabon da Najeriya ta samu afkuwar cutar.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Kimanin shakaru 40 ke nan rabon da Najeriya ta samu afkuwar cutar.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa mutum uku ne suka kamu da cutar kyandar biri a Najeriya.

Professor Isaac Odewole, Ministan Lafiya na Najeriya ya ce a cikin mutum 43 da ake zargin sun kamu da cutar kyandar biri, mutum uku ne kawai aka tabbatar sun kamu da cutar.

Ya bayyana hakan ne a taron manema labarai biyo bayan gwaje-gwajen da hukumar WHO ta yi a birnin Dakar a kasar Senegal.

A makon jiya an samu bulluwar cutar ne a jihohi takwas ciki har da babban birnin tarayya Abuja.

Kimanin shakaru 40 ke nan rabon da Najeriya ta samu afkuwar cutar.

Cutar ta samo asali ne daga jikin biri da sauran dabbobin kamar su bera da kurege da barewa.