Ɓarnar da girgizar ƙasa ta yi a Morocco cikin hotuna

Mummunar girgizar ƙasar da ta faru a kudancin Morocco, wadda ta hallaka dubban mutane, kuma ta lalata wuraren tarihi da yawa a Marrakesh.

Yanayin ya tilastawa 'yan wayon buɗe ido da dama da mutanen gari kwana a filin Allah-Ta'ala, saboda tsoron kada girgizar ta ci gaba.

fg

Asalin hoton, GETTY IMAGES

Bayanan hoto, Wata mata na duba ɓarnar da girgizar ƙasar ta yi a Marrakesh a dare Juma'a.
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Ɓurbishin wani gini mai tarihi da ya zubo kan wata mota, kuma abin ya rutsa da mutane masu yawa da lalata ababan hawa.
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Ɓarnan da girgizar ƙasar ta yi wa gine-gine ba su bayyana ba sai da gari ya waye a ranar Asabar
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Gine-gine da dama sun ruguje, abin da ya bar masu su cikin zullumi
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Girgizar kasar wadda ta kai maki 6.8 ta yi ƙamari ne a yankin Atlas Mountain mai nisan ƙasa da mil 50 daga cikin birni.
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Mutane a Marrakesh sun riƙa bayar da taimakon jini da ɗaruruwan jama'ar da musufar ta shafa
fg

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Da yawan mazauna birnin sun kwana ne a waje saboda fargabar abin da zai iya biyo bayan girgizar ƙasar
fg

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Gwamman mutane sun yi barci a kusa da wajen wanka da ke cikin totel a ɗaya daga cikin manyan otal ɗin yankin
Bayanan bidiyo, Yadda girgizar ƙasa ta lalata masallacin Kutubiyya