Koriya ta Arewa ta sake harba makamai

Wani daga cikin irin makaman da Koriya ta Arewa ke gwajin harbawa

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Koriya ta Arewa ta ce gwajin makaman gargadi ne ga 'yan-ina-da-yaki na makwabciyarta Koriya ta Kudu

Koriya ta Arewa ta yi gwajin harba wasu makamai masu linzami guda biyu, wadanda ba a gane sanfurinsu ba, zuwa cikin teku, kamar yadda hukumomin sojin koriya ta kudu suka bayyana.

Kasar ta harba makaman ne 'yan sa'o'i kadan bayan da ta ce a shirye take ta yi zaman tattaunawa kan batun kawar da makamanta na nukiliya da gwamnatin Amurka a karshen watan nan na Satumba.

Wannan shi ne wani kwakkwaran tayi na tattaunawa, tun bayan da ganawar Shugaba Trump da Kim Jong-un ta wargaje a Hanoi, babban birnin Vietnam a watan Fabrairu.

Kim Jong-un da 'yan jarida

Asalin hoton, EUROPEAN PHOTOPRESS AGENCY

Bayanan hoto, Mista Kim Jong-un na yi wa 'yan jarida bayani bayan duba wasu jiragen ruwan yaki na karkashin teku

Hadakar shugabannin rundunonin sojin Koriya ta Kudu da ta bayar da wannan sanarwa ta ce, an harba makaman masu linzami ne na Koriya ta Arewa daga wata tasha a lardin kudancin Pyongan, suka tashi zuwa cikin teku inda suka fada a yankin gabar gabas.

A kan hakan ne Koriya ta Kudu ta shiga wani taron gaggawa na tsaro domin sanin matakin da ta za ta dauka kan lamarin ganin yadda makwabciyar tata take ta irin wadannan gwaje-gwaje.

A 'yan watannin dai gwamnatin Koriya ta Arewa ta yi gwajin sabbin samfuran makamai masu linzami da ke cin gajeren zango, a don haka idan har wannan gwajin na yanzu ya tabbata, gaskiya to zai kasance na goma kenan da Pyongan din ta yi daga watan Mayu zuwa yanzu.

Wani makami mai linzami da Koriya ta Arewa ta yi gwajin harbawa

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, Kusan makamai masu linzami goma kenan Koriya ta Arewa ta gwada daga watan Mayu zuwa yanzu

Koriya ta Arewar ta kaddamar da wannan gwajin ne 'yan sa'o'i bayan da mataimakiyar ministanta na harkokin waje Choe Sun-hui ta fada a wata sanarwa cewa, gwamnatinsu a shirye take ta sake zaman tattaunawa da Amurka a wuraren karshen watan Satumbar nan.

Mr Trump and Mr Kim sun gana na dan lokaci a ranar 30 ga watan Yuni, amma har yanzu ba su sake zama ba

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Mista Trump da Mista Kim sun gana na dan lokaci a ranar 30 ga watan Yuni, amma har yanzu ba su sake zama ba

Ta ce taron zai iya kasancewa ne a lokaci da kuma wurin da bangarorin biyu suka amince.

Sai dai kuma Pyongyang din ta gargadi Washington cewa, akwai bukatar Amurkar ta zo da wata yarjejeniyar ta daban, ba kamar irin ta baya ba, idan ba haka ba tattaunawar za ta sake wargajewa.