Buhari da Atiku sun taya Super Falcons murna

Asalin hoton, CAf
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya taya Super Falcons nasarar lashe kofin Afirka a kasar Ghana.
Matan na Najeriya sun lashe kofin Afrika ne karo na uku a jare kuma karo na tara a tarihi bayan sun doke matan Afirka ta kudu Banyana Banyana ci 4-3 a fanareti.
Shugaban Najeriya ya taya Super Falcons murna a wani sakon da ya wallafa a Twitter.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
A cikin sakon, shugaban ya ce yana ma su murna sun tsallake zuwa gasar cin kofin duniya a Faransa a badi bayan sun lashe kofin Afirka karo uku kuma karo na tara a tarihi.
Dan takarar shugaban kasa a Jam'iyyar hamayya ta PDP Alhaji Atiku Abubakar shi ma ya taya Super Falcons murna a Twitter.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
Najeriya da Afrika ta kudu da kuma Kamaru ne za su wakilci Afirka a gasar cin kofin duniya da za a yi a badi a Faransa bayan sun zo matsayin na daya da na biyu da kuma uku a gasar cin kofin Afirka da aka kammala a Ghana






