Hare-haren Iran sun yi ajalin mutum ɗaya tare da jikkata wani a Isra'ila
Hukumar bayar da gajin gaggawa ta Isra'ila ta ce wani mutum ya mutu, yayin da wasu biyu kuma suka jikkata a tsakiyar kasar, a yayin da Iran ke ci gaba da kai hari a yankin.
Sojojin Ira'ila sun zargi Tehran da amfani da bama-bamai masu ƴaƴa. Wakiliyar BBC ta ce wannan ne karon farko da aka samu wani hari mai muni da Iran ta kai Isra'ila cikin kusan mako guda.
Na'urorin kare sararin samaniya na ƙungiyar ƙawancen tsaro ta Nato da ke gabashin tekun Mediterrian sun kakkabo wasu makamai masu linzami na Iran waɗanda suka shiga sararin samaniyar Turkiyya a karo na biyu.
Hukumomi a Bahrain sun ce aƙalla mutum talatin da biyu ne suka jikkata a wani harin da Iran ta kai a kudancin babban birnin ƙasar Manamah.
Qatar ma ta ce ta harbo wani makami mai linzami na Iran.