Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na 18 ga watan Maris 2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir da Aisha Aliyu Jaafar

  1. Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Asalin hoton, X/Bola Tinubu

    Bayanan hoto, Shugaban Najeriya Bola Tinubu

    Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a jihar Rivers bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.

    Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.

    A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.

    "Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al'ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.

    ''Na yi iyakar bakin kokarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.''

    Tinubu ya bayyana cewa babu wani shugaban ƙasa nagari da zai zura ido yana kallon abin da ke faruwa ba tare da bin matakan da kundin tsarin mulki ya tanada ba wajen ganin an shawo kan matsalar ta jihar Rivers.

    A cikin jawabin da ya gabatar ta kafafen talabijin na ƙasar, shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce: ''Bayan nazari kan halin da ake ciki a jihar Rivers, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999.

    "A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025."

    "Da wannan bayani, gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Mrs Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ƴanmajalisar dokokin jihar Rivers, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko."

  2. An tabbatar da kisan manyan jami'an Hamas biyar

    Ga jerin sunayen manyan jami'an Hamas biyar da aka tabbatar da mutuwarsu sanadiyyar ruwan wuta da Isra'ila ta yi a Gaza a cikin dare:

    • Yasser Harb, wakili a hukumar kula da harkokin siyasa ta Hamas, tare da iyalansa
    • Injiniya Issam Al-Da’alis, Shugaban hukumar kula da harkokin siyasa na Hamas
    • Manjo Janar Mahmoud Abu Watfa, ƙaramin ministan harkokin cikin gida na Gaza kuma babban jami'in tsaro na Hamas
    • Birgediya-Janar Bahjat Abu Sultan, Shugaban hukumar tsaron cikin gida ta Hamas, rundunar tsaro mafi tasiri ta ƙungiyar
    • Abu Omar Al-Hattah, ƙaramin ministan shari'a na Gaza

    Haka nan kuma ƙungiyar Palestinian Islamic Jihad (PIJ) - wata ƙungiya mai ƙawance da Hamas - ta tabbatar da mutuwar mai magana da yawunta, Naji Abu Seif, wanda aka fi sani da Abu Hamza.

  3. Ana zanga-zanga a Isra'ila kan ci gaba da kai hare-hare a Gaza

    Noga Kaplan
    Bayanan hoto, Noga Kaplan

    Isra'ilawan da ake garkuwa da ƴan'uwansu a Gaza sun gana da jagororin siyasa a majalisar dokokin Isra'ila da ke Jerusalem, yayin da wasu dandazon mutane ke zanga-zanga a waje.

    Lishi Lavie-Miran - wadda mata ce ga Omri Miram, mutumin da aka ɗauke a yankin Nahal Oz a ranar 7 ga watan Oktoba - ta faɗa wa ƴanmajalisar a cikin fushi cewar idan har aka kashe mijinta "kada a ɗora mata laifin abin da za ta aikata" idan wani ya nemi "zuwa kusa da ita".

    A wajen ginin majalisar, Samuel, wani sojan ko-ta-kwana kuma malamin tarihi, na daga cikin masu ɗaga murya suna neman a dawo da waɗanda ake garkuwa da su.

    Ya ce yana so ya zamo kyakkyawan misali ga ɗalibansa. "Shekarunsu 18, nan da wasu watanni za su shiga aikin soja kuma na yi amannar cewa bai kamata su shiga cikin irin wannan yaƙi ba," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa yana ganin akwai siyasa a cikin yaƙin: "Ba batun tsaron Isra'ila ba ne - Benjamin Netanyahu na da tasa manufar game da wannan yaƙin, kuma shi ba mutumin kirki ba ne. Ya kamata a dakatar da yaƙin nan kuma a dawo da mutanen da ake garkuwa da su gida."

    Noga Kaplan, mai shekara 22 a duniya ɗaliba ce a Jam'iar Hebrew, tana riƙe da allo wanda aka rubuta "Dole Bibi ya tafi".

    Ta ce ci gaba da yaƙin "shi ne abu mafi muni da zai faru ga waɗanda ake garkuwa da su" sannan ta yi kira ga gwamnatin Isra'ila da ƙungiyar Hamas da kuma Amurka da su ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta da kuma batun mayar da waɗanda ake garkuwa da su gida.

  4. Isra'ila ta ce za ta ci gaba da ruwan wuta a Gaza

    ...

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce za ta ci gaba da kai hare-hare ta sama a Gaza kamar yadda ta fara, wanda a sanadiyyar haka ne hukumomi a Gaza suka bayyana cewa sama da mutum 400 sun rasa rayukansu, ciki har da shugaban ɓangaren tsaro na Hamas.

    Tuni aka buƙaci dubban fararen hula da ke zaune a wasu yankunan Gaza su fice domin tsira da rayukansu.

    Isra'ila ta ce ta ɗauki matakin ne bayan Hamas ta ƙi amincewa da sharuɗɗan tsawaita matakin farko na tsagaita wuta a Gaza.

    Ƙungiyar Hamas a nata ɓangaren ta so ne a tafi kai-tsaye zuwa ga mataki na biyu na tsagaita wutar kamar yadda aka tsara.

    Ƙasashen duniya da dama sun yi tir da ruwan wutar da Isra'ila ta ci gaba da yi a yankin, duk da cewa an sanar da Amurka gabanin ci gaba da kai hare-haren.

  5. Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji

    Majalisar wakilan Najeriya

    Asalin hoton, BENJAMIN KALU

    Ƴan majalisar wakilan Najeriya sun amince da dokar haraji wadda ta ƙunshi ƙudiri guda huɗu da suka haɗa da ƙudirin dokar tafiyar da haraji da na kafa hukumar tattara haraji mai suna Nigeria Revenue Service da hukumar haɗaka ta tattara haraji da kuma ƙudirin haraji na Najeriya.

    Majalisar dai ta amince da ƙudirorin ne bayan an yi musu karatu na uku a ranar Talatar nan bayan yi wa ƙudrorin duban tsanaki ranar Alhamis ta makon da ya gabata.

    Kafin nan dai sai da kwamitin kuɗi na majalisar ya gudanar da jin ra'ayin jama'a kan batun, inda kuma ya tattara ra'ayoyin al'umma ya miƙa wa majalisar.

    A watan Okotoba ne shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike da ƙudirin dokar ga majalisar dokokin ƙasar.

  6. Wike ya ƙwace filin sakatariyar PDP a Abuja

    Ministan babban birnin Najeriya, Nyesom Wike, ya ƙwace wani fili mallakar sakatariyar Jam'iyyar PDP da ke Abuja.

    Jaridar DailyTrust ta ruwaito cewa kwace filin na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙar mai ɗauke da kwanan wata na 13 ga Maris 2025, wadda ta samu sa hannun shugaban sashen kula da filaye na babban birnin ƙasar, Chijioke Nwankwoeze.

    Nwankwoeze ya ce an yanke hukuncin ƙwace filin ne sakamakon gazawar babbar jam'iyyar adawar na biyan kudin gini na shekara shekara tun daga ranar 1 ga watan Janairun 2006 zuwa 1 ga watan Janairun 2025, duk kuwa da sanarwar da hukumar gudanarwar babban birni ta wallafa a jaridu da dama tun daga shekarar 2023 kan buƙatar biyan kuɗaɗen.

    Rahotanni dai na cewa filin na Jamiyyar PDP na daga cikin filaye 4,700 da ministan ya ƙwace a Abuja.

  7. Mun ɗora alhakin harin Isra'ila kan Amurka - Hamas

    A wata sabuwar sanarwa da Hamas ta fitar, ta ce Amurka ce ke da ''alhakin kisan gillar' da aka yi a Gaza bayan da ta bayyana cewa Isra'ila ta shaida wa Amurka shirinta na kai hare-haren gabanin kai harin.

    Sanarwar ta ce hakan ya ''tona asirin ƙaryar da suke yi na ikirarinsu kan damuwa da kawo ƙarshen yaƙin''.

    ''Muna buƙatar ƙasashen duniya su ɗauki matakin gaggawa na kama masu aikata laifukan yaƙi da masu goya musu baya'' in ji Hamas.

    A gefe guda kuma kafar yaɗa labarai da ke da alaƙa da Hamas, mai suna Filastin, ta ce an kashe jam'ian gwamnatin Hamas huɗu a hare-haren Isra'ila.

    Hazalika shugaban hukumar lafiya da Hamas ke jagoranta, Munir al-Barsh ya ce mutane fiye da 660 aka jikkata a hare-haren, kuma wasu da dama na ƙarƙashin ɓaraguzai.

  8. Farashin Zinare ya tashi sakamakon hare-haren Isra'ila a Gaza

    Zinare

    Asalin hoton, Getty Images

    Farashin Zinare a kasuwanni duniya ya yi tashin da ba a taɓa gani ba sakamakon rashin tabbas da ake samu a duniya wanda ya bunƙasa buƙatar zinaren.

    Farashin ya tashi zuwa fiye da dala 3,000 a ranar Talata a yayin da dakarun Isra'ila suka ƙaddamar da sabibin hare-hare a Gaza.

    Rikicin Gabas Ta Tsakiya da fargabar rikicin kasuwanci a duniya da kuma karyewar darajar dalar Amurka sun sanya farashin ya tashi da kaso 15 cikin 100 tun farkon shekarar.

    Masu sharhi na hasashen farashin zai ƙaru fiye da haka.

  9. Ƴar bautar ƙasa ta nemi afuwar al'ummar birnin Legas

    NYSC

    Asalin hoton, TWITTER/@NYSC_NG

    Wata ƴar Najeriya da ke yi wa ƙasa hidima (NYSC) a birnin Legas, wadda bidiyon ta ya karaɗe shafukan sada zumunta inda ta soki gwamnatin Tinubu kuma ta bayyana Legas a matsayin 'jiha mai wari', ta fito fili ta bada haƙuri kan kalaman nata na ƙasƙanci kan Legas.

    A shafinta na Instagram, ƴar bautar ƙasar ta amince cewa mai yiwuwa kalamanta ba su yi wa mazauna jihar daɗi ba, kuma ta bayyana nadamarta kan amfani da kalaman.

    Ta bayyana cewa ba ta yi niyyar zagin ƴan jihar ba, sai dai kawai tana bayyana abin da ta lura da shi ne a matsayinta na baƙuwa.

    Ta kuma ce kalaman nata wani yunkuri ne na fito da matsalolin Najeriya kullun na tsawon kwanaki 30 a jere domin fargar da alumma ke da ita kan matsalolin da ke addabar ƙasar kamar taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

  10. An sanya dokar hana fita sakamakon wani rikici a birnin Nagpur da ke Indiya

    An sanya dokar taƙaita zirga-zirga a wasu sassan birnin Nagpur da ke Indiya bayan wani rikici ya ɓarke sakamakon buƙatar wata ƙungiya na a cire kabarin wani jagoran addinin Musulunci da ya mutu fiye da shekaru 300 da su ka gabata.

    Masu fafutuka sun ce Aurangzeb, wani sarki a daular Mughal, ya musgunawa mabiya addinin Hindu.

    Masu zanga zangar sun ƙona wani hoton shi da kuma kabarinsa da aka kwaikwaya.

    Sun kuma ƙona motoci tare da lalata gidaje.

    Hukumomi a yankin sun haramta taro da ya wuce na mutane hudu, kuma sun ƙara tsaro a kusa da kabarin.

    Zuwa yanzu ƴansanda sun ce sun kama mutane fiye da hamsin.

  11. Mutane 50,000 sun rasa matsugunansu a Sudan ta Kudu - MDD

    Sudan ta Kudu

    Asalin hoton, AP

    Majalisar ɗinkin duniya ta ce mutum 50,000 sun rasa matsugunansu a Sudan ta Kudu sakamakon sabon rikicin siyasar da aka soma a ƙarshen watan da ya gabata.

    Shugabar da ke kula da ayyukan jinƙai na Majalisar a kasar, Anita Kiki Gbeho, ta ce mutane 10,000 sun tsere zuwa Habasha, kuma rikicin na kawo cikas ga ayyukan agaji.

    Sudan ta Kudu na fama da zazzafar adawar siyasa tsakanin shugaba Salva Kiir da tsohon jagoran ƴan tawaye Riek Machar, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙasa a yanzu a cikin gwamnatin haɗin gwiwa.

    Ana hasashen mutane aƙalla 400,000 ne aka kashe a yaƙin basasa da akayi tsakanin ɓangarorin biyu wanda ya zo ƙarshe bayan yarjejeniyar kafa gwamnatin haɗaka a 2018.

  12. Ɗimuwar rashin samun kujerar minista ce ke damun El-Rufai - APC

    El-Rufai

    Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta ce ɗimuwar rashin samun kujerar minista ce har yanzu ke damun tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai.

    Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Jam'iyyar ta fitar a matsayin martani ga kalaman tsohon gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai a hirarsa da BBC Hausa, inda ya ce jam'iyyar ta bar muradun da aka kafa ta akai wanda ya sa shi ficewa daga cikinta zuwa jam'iyyar SDP.

    "El Rufa'i ya faɗi ainihin dalilinsa na nuna damuwa, inda a cewarsu saboda bai ji daɗin yadda shugaba Tinubu da gwamnatinsa suka yi mishi ba kan batun rasa kujerar zama minista, kuma domin ya kare mutuncinsa, shi ne yake sukar jam'iyyar da ta kai shi ga nasara a siyasa." In ji sanarwar.

    Jam'iyyar ta ƙara da cewa ƴan Najeriya na da tunani fiye da yadda El Rufa'i ke musu kallo, kuma sun san cewa son kanshi kawai yake yi ba wai tsantsar damuwa kan ƙasar ba ne.

    Sanarwar ta kuma jam'iyyar APC ba ta damu da mataki ko kalaman El Rufa'i ba, kuma suna ci gaba da tarbar sabbin miliyoyin mutane masu shiga jam'iyyar a fadin ƙasar waɗanda ke shiga saboda muradun jam'iyyar masu kyau da kuma goya wa shugaba Tinubu baya kan tsare-tsarensa da ke kawowa ƙasar cigaba.

    APC ta kuma ce kiran da ya yi wa sauran ƴan adawa su shiga jam'iyyar SDP, ba komai ba ne illa tsantsar yaudara da ƙeta da kuma ƙoƙarin biyan buƙatun kai.

  13. MDD da wasu ƙasashen duniya sun yi alawadai da hare-haren Isra'ila a Gaza

    Shugabannin ƙasashen duniya sun fara tofa albarkacin bakinsu kan hare-haren baya-bayan nan da Isra'ila ta kai a Gaza da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 400.

    Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce ya 'kaɗu' da hare-haren, kuma ya yi kira da babbar murya da a mutunta yarjejeniyar tsagaita wutar.

    Firaminstan Australia Penny Wong ya ce ƙasarsa na buƙatar ɓangarorin biyu su mutunta tsagaita wutar, inda ya ce ''wajibi ne a kare dukkanin fararen hula''.

    Shi kuwa mataimakin Firaministan Belgium, Maxime Prevot, ya yi alawadai ne da hare-haren, inda ya yi kira ga duka ɓangarorin su tsaya kan yarjejeniyar, domin'' kar a koma gidan jiya''.

    Mai magana da yawun gwamnatin Rasha Dmitry Peskov shi ma ya bayyana lamarin a matsayin abin damunwa.

    A wani gefen kuma China ta ce ta ''damu matuƙa'' kan lamarin kuma tana fatan ɓangarorin biyu ba za su ɗauki wani mataki da zai ƙara ta'azzara lamarin ba, in ji mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen ƙasar Mao Ning.

  14. Ƴan sama jannati da suka maƙale a sararin samaniya sun kamo hanyar dawowa duniya

    ƴan sama jannati

    Asalin hoton, NASA

    Ƴan sama jannati biyu daga Amurka waɗanda suka maƙale a sararin samaniya na tsawon wata tara sun kama hanyar dawowa duniya.

    Kumbon da ke ɗauke da Butch Wilmore da Suni Williams ya samu nasarar baro sararin samaniyar a wata tafiya ta sa'o'i 17 zuwa gida.

    Tunda farko an sa ran tafiyar tasu zuwa sararin samaniya a watan Yunin 2024 za ta kwashe kwanaki takwas ne kacal, sai dai wasu matsaloli sun hana dawowarsu.

    Ana sa ran idan komai ya tafi yadda ake so, za su iso gaɓar tekun Florida a daren yau Talata.

  15. Sojojin Isra'ila sun umurci Falasɗinawa su fice daga wasu yankunan Gaza

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Dakarun Isra'ila sun bayar da sabbin umurnin ficewa daga wasu yankunan Zirin Gaza, saboda a cewarsu za a ci gaba da kai hare-hare.

    A yanzu haka bakiɗaya iyakar Zirin Gaza ya zama yanki mai mummunar hatsari, inda ake umurtar mutane su bar yankunan Beit Hanoun da Khuza'a da Abasan al-Kabira da kuma Al-Jadida.

    ''Su koma birnin Khan Younis da kuma yammacin Gaza cikin gaggawa'' in ji wani mai magana da yawun dakarun IDF a shafinsa na X

  16. Hotunan yadda hare-haren Isra'ila suka lalata wasu yankunan Gaza

    Hotunan ɓarnar da hare-haren Isra'ila na daren jiya suka yi a Gaza:

    Hare-haren Israila a Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Sansanin ƴan gudun hijira na Nuseirat da ke tsakiyar Zirin Gaza
    Hare-haren Israila a Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Makarantar Al-Tabeen a arewacin birnin Gaza
    Hare-haren Israila a Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Wata makaranta da aka mayar sansanin ƴan gudun hijira a Gaza
    Hare-haren Israila a Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Wani gida da aka lalata a harin daren jiya a Khan Younis da ke kudancin Gaza
  17. Ƴan tawayen M23 sun ce ba za su halarci tattaunawar sulhu ta yau a Angola ba

    Ƴan tawayen M23

    Asalin hoton, AFP

    Mayaƙan ƴan tawayen M23 sun ce ba zasu shiga shirin tattaunawar sulhu da gwamnatin Jamhuriyar Dimokardiyyar Kongo ba, wanda za ayi a yau Talata a ƙasar Angola bayan da Tarayyar Turai ta sanyawa mambobin ƙungiyar sabbin takunkumai.

    A cikin wata sanarwa, ƙungiyar ta M23 ta zargi wasu cibiyoyin ƙasashen duniya da ba ta bayyana sunansu ba, da yin zagon ƙasa ga yunƙurin samar da zaman lafiya.

    Jagoran ƙungiyar ta M23 Bertrand Bisimwa na cikin waɗanda aka sanyawa takunkumi.

    Tun da farko Rwanda ta katse duk wata hulɗar diflomasiyya da Belgium a kan taƙaddamar da suke yi kan cewa Rwandan na goyon bayan mayaƙan ƴan tawayen M23.

    Sai dai ministan harkokin wajen Belguim Maxime Prevot ya shaidawa BBC cewa matakin na Rwanda ba shawara ce mai kyau ba, saboda za ta yanke duk wata hulɗar diflomasiyya tsakaninsu.

    A ɗaya ɓangaren, gwamntin Kongo ta ce zata halarci tattaunawar duk da wannan koma baya da aka samu.

  18. Hare-haren Isra'ila sun kashe Falasɗinawa 330 a Gaza

    Gaza

    Asalin hoton, Getty Images

    Jiragen yaƙin Israila sun ƙaddamar da sabbin hare-hare ta sama a sassan zirin Gaza wanda shi ne hari mafi girma tun bayan da ta cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Hamas a watan Janairun daya gabata.

    Jami'ai a Gazan sun ce mutane aƙalla ɗari uku da talatin ne aka kashe, ciki harda wani babban jami'in Hamas na yankin, Mahmoud Abu Watfa.

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce Isra'ila za ta ci gaba da kai hare-haren har sai an saki dukkanin waɗanda aka yi garkuwa da su.

    Isra'ila ta kuma ce ta ɗauki wannan matakin ne saboda Hamas ta ƙi amincewa da shawarar tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta mataki na farko.

  19. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga nan sashen Hausa na BBC, inda za mu kawo muku labarai kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa Najeriya da ma sassan duniya.

    Ku leƙa shafukanmu na sada zumunta domin karanta wasu labaran da kallon hotuna da bidiyo da kuma yin muhawara.

    Ku kasance tare da mu.