KAI TSAYE, Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 11/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 11 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Iran na gudanar da jana'izar manyan kwamandojinta
  • Kotu ta ba mu damar ci gaba da tsare El-Rufai - ICPC
  • Iran ta yi barazanar kai hari kan bankunan Amurka da Isra'ila a Gabas ta Tsakiya
  • An kai hare-haren jirage marasa matuƙa kan wuraren Amurka a Iraq
  • Dangote ya rage farashin man fetur
  • Iran ta kai 'hari mafi muni' kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka
  • Amurka ta ce ta lalata jiragen Iran 16 masu sanya nakiyoyi a Hormuz
  • Za mu ɗauki duk wanda a fito zanga-zanga a matsayin maƙiyi - Iran
  • Me ya sa shugaban Iran ya nemi afuwar maƙwaftan ƙasar?

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. 'Hare-haren Isra'ila sun kashe aƙalla mutum 600 a Lebanon'

    Lebanon

    Asalin hoton, STR/EPA-EFE/REX/Shutterstock

    Isra'ila ta ce ta kaddamar da sabbin hare-hare kan Iran da Lebanon. Ta ce an kai hare-haren ne kan ababen more rayuwa a fadin Iran, da kuma wuraren da kungiyar Hizbullah ta ke a Beirut babban birnin Lebanon.

    Wakiliyar BBC ta ce rundunar sojin Isra'ila ta ce wasu hare-harenta na baya-bayan nan, ta kai su ne kan dakarun Iran da ke shirin harba makamai masu linzami zuwa Isra'ila.

    Ma'aikatar lafiya ta kasar Lebanon ta ce hare-haren da Isra'ila ke kai wa, zuwa yanzu sun kashe kusan mutum dari shida tun bayan fara yakin.

    Cikin daren jiya Talata, sojojin Amurka sun ce sun lalata wasu jiragen ruwan Iran goma sha shida da ke sanya nakiyoyin karkashin ruwa a mashigar Hormuz, bayan da shugaba Trump ya gargadi Tehran kan sanya nakiyoyin.

  2. Yanzu ne za mu soma hare-harenmu bayan na ramuwar gayya - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta bayyana cewa ta kawo ƙarshen salon hare-haren mayar da martani, inda ta ce daga yanzu za ta fara kai hare-hare ne kai tsaye maimakon ramuwar gayya.

    Mai magana da yawun hedikwatar rundunar sojin Khatam al-Anbiya, Ebrahim Zolfaqari, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa, inda ya ce "Iran ta kawo ƙarshen salon hare-haren mayar da martani, yanzu luguden wuta ne kawai za ta riƙa yi."

    Iran ta kuma bayyana cewa ba za ta bari ko lita ɗaya na mai ya wuce ta mashigar Mashigar Hormuz ba domin isa ga Amurka da Isra’ila da kuma abokan hulɗarsu ba.

    Zolfaqari ya ƙara da cewa duk wani jirgin ruwa ko tankar mai da ke kan hanyar zuwa Amurka ko Isra’ila ko abokan hulɗarsu za a kai musu hari.

    Haka kuma ya ce a shirya ganin farashin gangar mai ya kai dala 200, yana mai cewa farashin mai yana da alaƙa da tsaron yankin da ya zargi waɗannan ƙasashe da lalatawa.

  3. Miƙa wuyar maƙiyanmu kawai mu ke jira - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar juyin juya halin Iran IRGC ta ce abin da ta ke jira kawai shi ne maƙiyanta su miƙa wuya gaba ɗaya, tana mai jaddada cewa za ta dakatar da yaƙin ne kawai idan aka daina kai wa Iran hare-hare.

    A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce ta fara kashi na 38 na hare-haren da ta kira “True Promise 4.”

    Ta ce bayan wasu munanan hare-haren makamai masu linzami guda biyu da ƙasar ta kai lokaci guda kan sansanin jiragen saman Adiri a Kuwait, an kai mutane kimanin 100 da suka jikkata zuwa asibitocin Al Jaber da Al Mubarak na ƙasar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa rundunar ta kai farmaki kan wani sansanin Amurka da ke tashar jiragen ruwa ta Mina Salman a Bahrain ta hanyar amfani da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa.

    Haka kuma ta ce ta kai hari kan sansanin Patriot da wuraren ajiyar kayan aiki da cibiyoyin da sojojin Amurka ke zama a sansanonin ruwa na Muhammad al-Ahmad da Ali al-Salem da ke Kuwait, inda ta ce an yi musu mummunar barna.

  4. Ministan tsaron Najeriya ya gayyaci manyan hafsoshin tsaro

    ....

    Ministan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa mai ritaya, ya gayyaci duka manyan hafsoshin sojin ƙasar zuwa ofishinsa kan ƙaruwar hare‑haren ƴanbindiga a baya-baya nan kan sansanonin soji a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

    Taron wanda ke gudana a ma'aikatar tsaron ƙasar ya samu halartar babban hafsan tsaron ƙasar, Janar Olufemi Oluyede, da babban hafsan sojin ƙasa Laftanar Janar Waidi Shaibu.

    Sauran sun haɗa da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Sunday Aneke da babban hafsan sojin ruwa, Vice Admiral Idi Abass da wakilan Hukumar leƙen asiri ta Kasa (NIA) da wasu da dama.

    Rahotonni sun nuna cewa aƙalla manyan kwamandoji guda uku sun rasa rayukansu a hannun ƴanbindiga a Borno kwanan nan.

    Baya ga kwamandojin da suka mutu, dubban sojoji sun rasa rayukansu yayin da aka sace ɗaruruwan fararen hula.

    Gabanin fara taron, CG Musa ya ce sun yanke shawarar sake duba dabarun yaƙi da ‘yanbindiga duk da cewa rundunar.

  5. Me ya faru a kwana 10 na farkon yaƙin Amurka da Isra'ila a kan Iran?

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Ga wasu daga cikin jerin abubuwan da suka faru a kwana 10 na farkon yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran.

    • Amurka da Isra'ila sun ƙaddamar da hare-hare a kan Iran ranar 28 ga watan Fabrairu, inda suka hari cibiyoyin makaman nukiliya da shugabannin kasar.
    • Hare-haren sun kashe Jagoran Addinin Kasar, Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya jagoranci kasar tun 1989.
    • Iran ta mayar da martani ta hanyar kaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan Isra'ila da kasashen Gabas ta Tsakiya. Ta kira hare-haren Amurka da Isra'ila da “tsokana”.
    • Iran ta zargi Amurka da Isra'ila da kai hari wata makarantar yan mata, inda aka kashe mutum 168.
    • Amurka da Isra'ila ba su dauki alhaki ko musa hannunsu a harin ba
    • Kazalika, yakin ya ɗauki sabon salo bayan da Hezbollah ta kaddamar da hare-hare kan Isra'ila daga Lebanon.
    • Amurka da Isra'ila sun kaddamar da sabbin hare-hare a Iran, musamman kan wuraren ajiye mai.
    • An zabi Ayatollah Mojtaba Khamenei a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa a matsayin Jagoran Addini a ranar Lahadi.
  6. Gwamnatin Najeriya ta fara kwashe 'yan ƙasarta daga Iran

    ...

    Asalin hoton, Tinubu/X

    Gwamnatin Najeriya ta fara kwashe 'yan ƙasar daga ƙasar Iran da suka nuna buƙatar a dawo dasu gida, tare da raka su ta kan iyakar ƙasar Armeniya domin tabbatar da tsaron lafiyarsu a yayin da ake ci gaba da samun tashe-tashen hankula a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Shugabar hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje NiDCOM, Abike Dabiri-Erewa, ce ta bayyana hakan a wani sako da ta wallafa a shafinta na X a jiya Talata.

    Shugabar ta kuma tabbatar da cewa kawo yanzu babu wani ɗan Najeriya a Iran da rikicin da ke faruwa ya shafa, inda ta ce jami’an ofishin jakadancin suna can a bakin iyakar ta Iran da Armenia domin karɓar da kuma taimakawa waɗanda ke son a kwaso su daga Iran su tsallaka iyakar.

    Dangane da soma tasowar jiragen da za a dawo da su gida kuwa, Shugabar ta ce a halin yanzu sararin samaniyar yankin ba shi da tsaro, amma ta tabbatar wa ‘yan Najeriya mazauna yankin Gabas ta Tsakiya cewa, tawagar gwamnatin tarayya na shirye-shiryen kwaso su.

    Ta ce, "an fara samun jirgin da ya taso daga ƙasar Hadaddiyar Daular Larabawa zuwa Legas kwanaki biyu da suka gabata kafin wani sabon hari da ya sa aka rufe sararin samaniyar kasar."

    Ta ƙara da cewa "da zarar an bude sararin samaniyar, tawagar gwamnatin tarayya da ta ƙunshi jami’ai daga ma’aikatu daban-daban za su shiga aikin kwaso mutanen."

    Wannan matakin da ya biyo bayan ƙaruwar rikicin da ya fara tun daga ranar 28 ga watan Fabrairu bayan wani harin soji da Amurka da Isra'ila suka kai kan Iran.

  7. Qatar ta ce ta kakkaɓo makami mai linzami da Iran ta harba mata

    Gwamnatin Qatar ta sanar da cewa sojojin ƙasar sun kakkaɓo wani makami mai linzami da Iran ta kai mata hari da shi kafin ya kai ga haddasa lahani.

    Ministan tsaro ya bayyana cewa an harba makamai masu linzami daga Iran, amma sojojin Qatar sun yi nasarar kakkaɓo dukkan makaman kafin su faɗa ƙasar.

    Babu rahoton wasu raunuka ko lahani ga kadarori.

    Wannan sabon lamari ya zo ne yayin da rikicin yankin ke ƙara tsanani, inda Iran ke amfani da makamai wajen kai hari a yankin Gabas ta tsakiya da ke dauke da sansanin sojojin Amurka.

  8. Isra’ila ta ƙaddamar da sabbin jerin hare‑hare kan Lebanon da Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Isra’ila ta sanar da cewa ta kai sabbin hare-hare a kan yankunan Iran da kuma Beirut, Lebanon inda harin ya nufi ababen more rayuwa na ƙungiyar Hezbollah da kuma wasu wuraren da ta ce na gwamnatin Iran.

    Wannan ya biyo bayan rikicin da ke ƙara tsananta tsakanin Isra’ila da rundunar Hezbollah da kuma yaƙin da ke ci gaba tsakanin Isra’ila da Iran a yankin Gabas ta tsakiya.

  9. Iran na gudanar da jana'izar manyan kwamandojinta

    ....

    Asalin hoton, GETTY/ATTA KENARE

    Iran na gudanar da jana’izar wasu manyan kwamandojinta a Tehran waɗanda suka rasa rayukansu a hare‑haren da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar a ƙasar.

    A cewar wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar ta ce gawarwakin manya sojojin waɗanda ta kira 'gungun mushahidan yaƙin Ramadan' za a binne su ne a 'maƙabartar mushahidai' ta ƙasar.

    Sanarwar ta ce daga cikin kwamandojin da suka rasu, akwai: Abdolrahim Mousavi, Shugaban Ma’aikatar Sojojin da Mohammad Pakpour, Kwamandan dakarunJuyin Juya Halin Iran da Ali Shamkhani, Sakataran Majalisar Tsaro da Aziz Nasirzadeh, Ministan Tsaro da Mohammad Shirazi, Shugaban Ofishin Kwamandan Sojojin da kuma Mohsen Darehbaghi da dai sauransu.

    Bugu da ƙari, al’umma da ke halartar jana’izar suna kallon wannan lokaci a matsayin rana ta tunawa da jarumtaka da sadaukarwa.

    Rikici dai na ƙara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya a yayin da Iran da Amurka da Isra'ila ke ci gaba da kai wa junansu hare-hare.

  10. Kotu ta ba mu damar ci gaba da tsare El-Rufai - ICPC

    E-Rufai

    Asalin hoton, KDGOV

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC a Najeriya ta ce kotu ta ba ta umarnin ci gaba da tsare tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir el-Rufai, har na tsawon ƙarin kwanaki 14.

    Jaridar The Nation a Najeriya ta ambato hukumar na cewa kotun ta ba ta damar ne domin samun isasshen lokacin kammala binciken da ake yi a kan zarge-zargen da ake wa El-Rufai inda yanzu akwai sabbin zarge-zarge na cin hanci da rashawa da wasu laifuffuka da ake zargin tsohon gwamnan da su.

    An bayar da wannan umarni ne a ranar Alhamis a gaban lauyan El-Rufa'i, kuma zai ƙare a ranar 19 ga Maris, kamar yadda ICPC ta bayyana

    Lauyan tsohon gwamnan dai ya shigar da buƙatar soke wannan umarnin a Babbar Kotun Majistare ta Bwari dake Abuja, inda ya yi ƙoƙarin gabatar da hujjoji da dama domin tabbatar da cewa ba a bi ƙa’ida wajen tsare El-Rufai ba, sai dai kotu ta nuna cewa har yanzu akwai buƙatar a ci gaba da tsarewar har sai an kammala binciken.

    Babban Mai Shari’a na Majistare, Okechukwu John Akweke, ya saka ranar 17 ga Maris don yanke hukunci ko za a soke wannan sabon umarnin tsare.

  11. Iran ta yi barazanar kai hari kan bankunan Amurka da Isra’ila a Gabas ta Tsakiya

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani mai magana da yawun Khatam al-Anbiya, babban kwamiti na hadin gwiwar sojin Iran, ya yi barazanar cewa Iran za ta kai hari kan bankunan Isra’ila da na Amurka a yankin a matsayin ramuwar gayya ga abin da ya ce 'an kai hari kan wani banki a Iran'.

    Ebrahim Zolfaghari ya gargaɗi cewa “mutane a yankin kada su kusanci bankuna daga nisan kilomita ɗaya,” kamar yadda gidan talabijin na gwamnatin Iran, IRNA, ya ruwaito.

    “Abokan gaba sun ba mu ‘yancin kai hari kan cibiyoyin tattalin arziki da bankuna” mallakar Amurka da Isra’ila, in ji Zolfaghari.

    Haka kuma,IRNA ta ruwaito cewa an kai hari kan wani gini na Bankin Sepah, bankin gwamnati dake Tehran.

    A ranar Talata, kafafen watsa labaran Iran sun ruwaito cewa an samu wasu matsaloli a ayyukan Bankin Sepah da wani bankin gwamnati me suna Melli.

  12. An kai hare-haren jirage marasa matuƙa kan wuraren Amurka a Iraq

    An kai hare-hare da jirage marasa matuƙa kan wasu wuraren Amurka a Iraq, ciki har da wani babban ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Bagadaza a ranar Talata.

    Rahotanni sun ce harin bai jikkata kowa ba, kuma ana zargin ƙungiyoyin mayaƙa da Iran ke mara wa baya ne suka kai harin.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wani saƙon gargaɗi na cikin gida na Amurka da jaridun Washington da Reuters suka ruwaito.

    Jaridar Washington Post ta ce an harba jirage marasa matuƙa guda shida zuwa wurin, amma jami’an tsaro sun kakkaɓo guda biyar daga cikinsu.

    A arewacin Iraq kuma, an kakkaɓo aƙalla jirage marasa matuƙa guda uku a wajen birnin Erbil da ke yankin Kurdistan mai cin gashin kai, ba tare da samun rahoton asarar rai ba.

    Akwai wani sansanin sojojin Amurka kusa da filin jirgin saman Erbil, kuma birnin na daga cikin wuraren da hare-haren Iran da ƙungiyoyin da ke goyon bayanta suka fi kai hari a baya-bayan nan.

  13. Dangote ya rage farashin man fetur

    ...

    Asalin hoton, X/@AlikoDangote

    Matatar man Dangote ta sanar da rage farashin man fetur daga naira 1,175 kan kowace lita zuwa naira 1,075 wato ragin naira 100 kenan.

    Wata sanarwa da matatar ta fitar a shafinta na X ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan saukar farashin danyen mai a kasuwannin duniya kuma anyi hakan ne bisa tsarin sabon farashi da kamfanin ya fitar.

    Sanarwar ta kuma bayyana cewa matatar ta rage farashin man dizal zuwa naira 1,430 kan kowace lita daga tsohon farashin naira 1,620.

    Matatar ta jaddada ƙudurinta na taimakawa wajen karfafa tsaron makamashi a Najeriya tare da la’akari da halin tattalin arzikin da ‘yan kasar ke ciki in ji babban jami'in.

    Wannan shi ne karo na farko da aka rage farashin bayan ƙarin sau uku a jere da aka yi a makonnin baya wanda ya sa farashin man ya yi matukar tashi.

  14. Za mu ɗauki duk wanda ya fito zanga-zanga a matsayin maƙiyi - Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban 'yan sandan Iran ya yi gargaɗin cewa za a ɗauki duk wanda aka gani yana zanga-zangar nuna ƙin jinin gwamnatin ƙasar a matsayin abokin gaba.

    Ahmad-reza Radan ya ce a shirye jami'ai suke su su hukunta duk wani ɗan koren ƙasashen waje, a wani shaguɓe ga Amurka da Isra'ila.

    A halin yanzu dai, wasu Iraniyawa da basa goyon bayan gwamnati da suka samu aikowa BBC saƙonninsu, sun ce sun gaji da jin hare-haren bama-bamai.

    Jami'an Iran sun ce an kashe mutane sama da dubu daya da dari uku tun da aka fara yakin.

  15. Amurka ta ce ta lalata jiragen Iran 16 masu sanya nakiyoyi a Hormuz

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka ta ce ta lalata jiragen ruwan Iran goma sha shida da ke sanya nakiyoyin ƙarkashin ruwa a mashigin Hormuz, wata hanya mai muhimmanci ta fitar da kashi 20 na makamashin da ake amfani da shi a duniya.

    Bataliyar rundunar sojin Amurkar da ke gabas ta tsakiya ta walafa wani bidiyo da ke nuna yadda ake kai wa jiragen hari tare da lalata su.

    Wannan ya zo ne bayan da Shugaba Trump ya gargaɗi Iran game da sanya nakiyoyi a mashigin da zummar hana zurga zurgar jiragen ruwa.

    Kafin hakan fadar White House ta karyata batun rakiyar wasu jiragen ruwa masu dauke da mai ta cikin mashigin na Hormuz, da sakataren Makamashin kasar Chris Wright ya wallafa cewa sojojin kasar sun yi.

  16. Mojtaba Khamenei: Daga shekaru a bayan fage zuwa zama jagoran addinin Iran

    ....

    Asalin hoton, Getty Images, BBC

    Ana tsaka da shirye-shirye ne a tashar talabijin ta gwamnatin Iran sai aka dakata, inda aka ce akwai sanarwa mai matuƙar muhimmanci.

    A lokacin ne mai gabatar da shirye-shiryen ya tabbatar da naɗa Mojtaba Khamenei, ɗan tsohon jagoran addinin Iran Ali Khamenei a matsayin sabon Ayatollahi na ƙasar.

    An fitar da sabon jagoran addinin ne kimanin kwana takwas bayan an kashe Ali Khamenei a hare-haren Amurka da Isra'ila a Iran, wanda aka fara a ranar 28 ga watan Fabrairu.

    Kisan tsohon jagoran addinin ya matuƙar girgiza ƙasar Iran, wadda ta koma Jamhuriyar Musulunci bayan juyin-juya-halin shekarar 1979.

    An gudanar da zaɓen sabon jagora addinin ne a cikin sirri, matakin da majalisar shura mai mutum 88 ta ɗauka.

  17. Iran ta kai 'hari mafi muni' kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan wasu sansanonin sojin Amurka da ke Gabas ta Tsakiya, kamar yadda wata sanarwa daga rundunar juyin juya halin Iran ta bayyana a shafin X.

    Sanarwar ta ce an harba makamai zuwa sansanin Al Udeid da ke Qatar, da sansanin Arifjan a Kuwait, da kuma sansanin Harir a Iraƙi.

    Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Iran, ISNA, ya ce harin mai yawa da aka ƙaddamar ya kuma nufi rundunar ruwa ta biyar ta Amurka da ke yankin, inda aka ce wasu muhimman kayayyakin aikin sojojin Amurka sun lalace.

    A wani sako na daban, an bayyana harin a matsayin mafi girma kuma mafi muni da Iran ta kai tun bayan fara wannan rikici.

    Sai dai zuwa yanzu jami’an Amurka ba su fitar da wata sanarwa ba kan lamarin.

    A lokaci guda kuma an ji kuwwar na’urorin gargadi a sassa da dama na Isra’ila bayan wani sabon harin makamai masu linzami da Iran ta kai, wanda gidan talabijin na Isra’ila ya bayyana a matsayin mafi muni tun soma yakin.

    Isra’ila ta ce garkuwar tsaron sararin samaniyarta ta kakkabo makamai da dama.

    Rundunar juyin juya halin Iran ta ce ta kai harin ne kan wata cibiyar sadarwa ta tauraron dan adam a Haifa da ke arewacin Isra’ila, tare da wasu sansanonin soji.

    Iran ta kuma yi ikirarin kai hari kan wasu sansanonin sojin Amurka a yankin, ciki har da wurare a Kurdistan na Iraƙi da Bahrain, tare da rahotannin wasu hare-hare a Hadaddiyar Daular Larabawa da Saudiyya.

    Matakin Iran na faɗaɗa hare-haren zuwa ƙasashen da ke da alaƙa da Amurka na iya yin tasiri mai yawa ga tattalin arzikin duniya.

  18. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Laraba.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

    Aisha Babangida ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.