Ana zargin Abiy Ahmed da hana shigar da kayan agaji sansanin ƴan gudun hijra a Tigray
Jam'iyya mai mulkin yankin Tigray na Habasha ta zargi gwamnatin Abi Ahmed da hana shigar da agaji sansanonin 'yan gudun hijira.
Jam'iyyar TPLE ta ce ci gaba da hakan na barazana ga dubban 'yan gudun hijirar da ke tsananin bukatar taimako, wadanda yunwa ta tagayyara. Kuma hakan ya take yarjejeniyar Pretoria da aka cimma ta kawo karshen yakin shekaru biyu a yankin na Tigray.
Ta kara da cewa kusan 'yan gudun hijira miliyan daya ba za su iya komawa yammacin Tigray ba, wanda sukai ikirarin gwamnatin Habasha ce ke iko da shi.
TPLF ta yi kira ga kwamitin tsaro na MDD da kungiyar Tarayyar Afurka su sa baki kan lamarin.