Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Laraba 26/11/2025

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Laraba 26/11/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Isiyaku Muhammad, Aisha Aliyu Jaafar da Ibrahim Yusuf Mohammed

  1. 'Rasha ba ta shirya tattaunawar zaman lafiya da Ukraine ba' - von der Leyen

    Ursula von der Leyen

    Asalin hoton, EPA

    Shugabar hukumar tarayyar Turai Ursula von der Leyen ta bayyana halin da ake ciki a yaƙin Ukraine a matsayin "mai cike da tashin hankali" kuma "mai matuƙar hatsari" tare da zargin Rasha da cewa ba ta da niyyar shiga tattaunawar sulhu.

    Kalaman na ta sun zo ne jim kaɗan kafin mai magana da yawun Kremlin Dmitry Peskov ya ce "ya yi wuri" a fara maganar ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya.

    Von der Leyen ta ce Ukraine za ta buƙaci ƙwaƙƙwaran tabbacin tsaro da zai iya hana aukuwar duk wani hari nan gaba, ta na mai cewa har yanzu Rasha na tunani irin na zamanin yaƙin duniya na biyu kuma tana kallon nahiyar Turai a matsayin wurin da za ta iya mamayewa.

    Ta yi jawabi ne a Majalisar tarayyar Turai a Strasbourg yayin da Amurka ta ƙara zage damtse wajen tabbatar da yarjejeniya tsakanin Kyiv da Moscow.

    Bayan tattaunawar da aka yi a wannan makon a Geneva da kuma Abu Dhabi, Ukraine ta amince da wani daftarin yarjejeniyar zaman lafiya, bayan da aka yi kwaskwarima kan wani shiri na farko da ke kunshe da sharuɗɗa 28, wanda ya sha suka bayan an yi zargin cewa ya fifita muradun Rasha.

    Shugaban Ukraine Vlodymyr Zelensky ya ce sabon daftarin yana nuni da "hanyar da ta dace" - amma har yanzu akwai manyan batutuwan takaddama da Rasha kuma Kremlin ta yi watsi da batun cewa an kusa sasantawa.

  2. Lebanon ba za ta zauna lafiya ba har sai mun tabbatar da tsaronmu - Isra'ila

    Labanon

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan tsaron Isra'ila ya ce Labanon ba za ta zauna lafiya ba har sai an tabbatar da tsaron ƙasarsa.

    Mista Israel Katz ya bayar da misali da kisan da Isra'ila ta yi wa jagoran ƙungiyar Hezbollah, Haytham Ali Tabatabai a wani harin da ta kai birnin Beirut, inda ya ce Isra'ila za ta zafafa kai hare-hare har sai ta karya lagon mayaƙan ƙungiyar da ta ce na ɗauke da makamai.

    A baya dai Isra'ila da Hezbollah sun cimma yarjejeniyar tsagaita wuta bayan kwashe fiye da shekara ɗaya suna kai wa juna hari.

    Amma duk da haka Isra'ila ta ci gaba da kai wa yankunan Lebanon jerin hare-hare.

    Majalisar Dunkin Duniya ta ce a ɗan wannan tsakani Isra'ila ta kashe fararen hula 127 ƴan Labanon, inda ta nemi a gudanar da bincike.

  3. Majalisar dattawan Najeriya ta nemi a fara yankewa masu satar mutane hukuncin kisa

    Nigerian Senate

    Asalin hoton, Nigerian Senate/Tope Brown

    Majalisar dattawan Najeriya ta zartar da wani ƙudiri da ta ayyana satar mutane a matsayin aikin ta'addanci, inda ta tanadi cewa a yi gyara ga dokar ta'addanci domin zartar da hukuncin kisa kan waɗanda aka samu da laifin aikata satar mutane.

    An zartar da wannan ƙudurin ne yayin zaman majalisar a ranar Laraba.

    A ƙarƙashin sabuwar dokar, a cewar majalisar, da zarar an tabbatar da laifin yin garkuwa da mutane, dole ne a aiwatar da hukuncin kisa.

    Najeriya na fama da matsalar tsaro da ake ci gaba da ruruwa sakamakon hare-haren da ƙungiyoyin ƴan bindiga ke kai wa a ƙauyuka da kashe mutane da kuma sace mutane domin neman kuɗin fansa.

    Dangane da batun sace-sacen da ƴan ta’adda suka yi a baya-bayan nan, shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ba da umarnin a killace dazuzzukan jihar Kwara baki ɗaya.

  4. Adadin waɗanda su ka mutu a gobarar Hong Kong ya kai 36

    Hong Kong Blaze

    Asalin hoton, Reuters

    Aƙalla mutane 36 ne suka mutu sakamakon babbar gobarar da ta laƙume wasu manyan gine-gine a gundumar Tai Po ta Hong Kong.

    Akwai rahotannin da ke cewa wasu mazauna garin da dama sun maƙale a ginin, kuma ƴan sanda sun ce mutane 279 sun bace.

    Sama da jami’an hukumar kashe gobara 760 ne aka tura domin shawo kan gobarar da ta tashi a ranar Laraba da yamma, inda hotuna ke nuna wuta da kuma hayaki mai launin toka da ke ta turnuke yankin ya kuma mamaye sararin samaniyar birnin.

    Ba a san musabbabin tashin gobarar ba, amma ana tunanin cewa ta bazu cikin sauri saboda itatuwan gwangwala da aka sanya a jikin ginin ta waje sakamakon gyara da ake yi.

    Jami’an hukumar kashe gobara sun ce tun farko mutane tara ne suka mutu a wurin, yayin da wasu huɗu kuma suka mutu a asibiti.

    Daga cikin waɗanda suka mutu har da ma'aikacin kashe gobara Ho Wai-ho, mai shekara 37.

    Zafin wutar da gobarar da kuma tarkacen da ta haifar sun kawo cikas ga aikin ceto.

  5. An tabbatar da hukuncin ɗaurin shekara 27 kan tsohon shugaban Brazil

    Jair Bolsonaro

    Asalin hoton, Reuters

    Kotun ƙolin Brazil ta umarci tsohon shugaban ƙasar Jair Bolsonaro ya fara zaman gidan yari na tsawon shekaru 27 da watanni uku bisa samunsa da laifin yunƙurin juyin mulki bayan ya sha kaye a zaɓen da ya gabata.

    Mai shari’a Alexandre de Moraes ya yanke hukuncin cewa shari’ar ta kai ga yanke hukuncin ƙarshe kuma ba za a sake ɗaukaka ƙara ba.

    Bolsonaro, mai shekara 70, an same shi da laifin jagorantar wata maƙarƙashiya da nufin ci gaba da mulki bayan ya sha kaye a zaɓen 2022 a hannun abokin hamayyarsa, Luiz Inácio Lula da Silva.

    Zai kasance ne a gidan yarin ƴan sandan tarayya da ke Brasilia, babban birnin ƙasar, inda ake tsare da shi tun ranar Asabar ɗin da ta gabata.

  6. Labarai da dumi-dumi, Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a Najeriya

    Bola Tinubu

    Asalin hoton, State House

    Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, yana mai bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami'an 'yansanda da na soja.

    Shugaban wanda ya bayar da umarnin yayin wani jawabi a fadarsa, ya bai wa rundunar 'yansandan ƙasar umarnin ɗaukar ƙarin jami'ai 20,000.

    Ya ce adadin sababbin jami'an da za a ɗauka yanzu ya zama 50,000, bayan umarnin da ya bayar ranar Lahadi na ɗaukar 30,000.

    Ɗaya daga cikin mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa, Abdulaziz Abdulaziz, ya faɗa wa BBC cewa dokar na nufin ɗaukar matakan gaggawa domin shawo kan matsalar tsaro a faɗin Najeriya.

    Kazalika, shugaban ya bai wa hukumar 'yansandan farin kaya ta DSS umarnin ɗaukar ƙarin jami'ai a rundunar kare dazuka ta Forest Guard.

    Shugaba Tinubu ya kuma umarci DSS ta aika dakarun Forest Guard "domin zaƙulo 'yanta'adda da 'yanfashi daga dazuka".

    "Babu wani sauran gidan ɓuya ga miyagu," in ji shi kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ta bayyana.

  7. Rundunar yansandan Abuja ta ƙaddamar da shirin daƙile matsalar tsaro

    Nigeria Police

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar ƴansandan babban birnin tarayya (FCT) ta kafa wani shirin inganta tsaro ta haɗin gwiwa a Abuja da aka fi sani da “Operation Sweep FCT”.

    An ƙaddamar da shirin ne a hukumance a ranar Talata, 25 ga Nuwamba, 2025, tare da goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya Nyesom Ezenwo Wike.

    A cikin wata sanarwa da jami'ar hulɗa da jama'a ta rundunar, Josephine Adeh ta wallafa a shafin rundunar ta X, wannan na zuwa ne a matsayin wani mataki da ke da nufin samar da ingantaccen tsaro ga mazauna babban birnin ƙasar.

    Sanarwar ta ƙara da cewa, “Rundunar ƴansandan babban birnin tarayya (FCT) tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro sun sake farfaɗo da aikin tsaro na haɗin gwiwa mai suna ‘Operation Sweep FCT.

    “Kafin a tura jami’an tsaro zuwa sassan babban birnin tarayyar, shugabannin hukumomin tsaro da ke birnin sun yi jawabi ga jami’an a dandalin Eagle Square, inda suka jaddada ma su buƙatar inganta aikin tsaro, ta hanyar amfani da bayanan sirri.''

    Sanarwar ta kuma ce “Don tabbatar da ingantaccen aikin tsaro, an raba birnin zuwa yanki-yanki, wanda zai bayar da damar gudanar aiki cikin sauri, ta hanyar inganta sintiri a duk gundumomi da al'ummomi.

  8. Sojoji sun ce sun karɓe mulki a Guinea-Bissau

    Guinea Bissau

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu jami'an soji sun ce sun ƙwace cikakken iko da ƙasar Guinea-Bissau a daidai lokacin da rahotanni ke cewa an kama shugaban ƙasar Umaro Sissoco Embaló.

    Jim kaɗan bayan an ji ƙarar harbe-harbe a Bissau babban birnin ƙasar, majiyoyin gwamnati sun shaida wa BBC cewa an tsare Embaló.

    Daga nan sai jami’an soji suka bayyana a gidan talabijin na ƙasar, inda suka ce sun dakatar da gudanar da zaɓen ƙasar da aka gudanar kuma za su ci gaba da tafiyar da harkokin ƙasar.

    Al'ummar ƙasar ta yammacin Afirka na dakon sakamakon zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata, inda aka hana dan takarar jam'iyyar adawa tsayawa takara.

    A ranar Alhamis ne ake sa ran sakamakon kuma Embaló da abokin hamayyarsa Fernando Dias sun yi iƙirarin nasara.

    Janar Denis N'Canha, shugaban sojoji na fadar shugaban ƙasa, ya karanta wata sanarwa da ta ayyana kwace mulki tare kuma da rufe iyakokin ƙasar.

    Janar N'Canha ya umurci jama'ar ƙasar da su "kwantar da hankulansu".

    Baya ga Embaló, an kama hafsan sojojin shugaban ƙasa da wasu ministoci da dama.

  9. Ƴaƴan tsohon shugaban Nijar sun buƙaci a saki mahaifinsu bayan fiye da shekaru 2 a ɗaure

    Mohammed Bazoum

    Asalin hoton, EPA

    Ƴaƴan tsohon shugaban Jamhuriyar Nijar Mohammed Bazoum sun sake yin kira ga gwamnatin mulkin soja da ta saki mahaifinsu yayin da ya cika watanni 28 a tsare.

    A yau ne dai hamɓararen shugaban ƙasar tare da mai ɗakinsa suke cika shekara biyu da wata uku a rufe a wani ɓangare na fadar shugaban ƙasa tun bayan juyin mulkin ranar 26 ga watan Yulin 2023.

    Ƴaƴan shugaban ƙasar da suka ce tun wannan lokaci basu gana da mahaifan nasu ba, inda suka yi kira ga ƙasashen duniya da su sa baki a kawo ƙarshen wannan tsarewa da ake ci gaba da yi wa mahaifansu.

    Cikin sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar, sun bayyana halin ƙunci da mahaifansu ke ciki, waɗanda suka ce ke illa ga lafiyarsu.

    ''Ba sa ganin hasken rana, ba su motsawa ko tafiya, babu mai kai musu ziyara''. kamar yadda ɗaya daga cikin ƴaƴansa Hinda Bazoum ta shaidawa BBC. ''Muna buƙatar kamar dukkanin yara mu rayu tare da iyayenmu''.

    Sun kuma ce dukkanin matsalolin tsaron da sojojin suka ce su ne dalilin su na yi juyin mulki, ba a lokacin mahaifinsu aka soma ba.

    Ƴaƴan tsohon shugaban ƙasar sun kuma ce mahaifinsu bai taɓa kira ga ƙasashen duniya su kawo hari ƙasar domin a ceton shi ba, don haka suna neman a yi musu adalci tare da daina zargin su da laifin da ba su aikata ba.

    Wannan ne dai karo na farko da ƴaƴan shi ke fitar da sanarwar haɗin gwiwa inda suke kiran ƙasashen duniya su kawo masu ɗauki.

  10. Za a shirya fim ɗin rayuwar Nana Asma'u ɗiyar Usman bin Fodiyo

    .

    Asalin hoton, HON BELLO IDRIS

    Majalisar Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar III da ma’aikatar masana’antu da kasuwanci da saka hannun jari ta tarayya sun amincewa kamfanin Script Plus Limited shirya wani fim na rayuwar Nana Asma’u 'yar Shehu Usman Bin Fodiyo.

    Za a dai yi Fim din ne domin irin gudunmawar da Asma’u, ‘yar wanda ya kafa Daular Sakkwato, wato Usman dan Fodio ta bayar a ɓangaren ilimi, da ƙarfafa mata da kuma ilimin addinin Musulunci.

    Hajiya Rahama Abdulmajid, mai bayar da shawara ta musamman kan harkokin rediyo da yada labarai, a ofishin mataimakin shugaban Najeriya, wadda ke jagorantar shirya fim din ta ce za a shirya shi ne saboda halin da arewacin Najeriya ya tsinci kansa musamman a fannin ilimi.

    Ta ce mata na fuskantar barzana wajen neman ilimi, wanda ya sa suka ga muhimmancin bayar da labarin Nana Asmau.

    Rahama Abdulmajid ta kuma ce akwai buƙatar duniya ta san cewa tun shekara 200 akwai wanna ƙokari na ilmantar da yara mata.

    Ta ƙara da cewa bayan samun sahalewar Majalisar Sarkin Musulmai, za a soma daukar fim ɗin gadan gadan, kuma zuwa shekara mai zuwa za a soma haska fim shi.

    Ta kuma bayar da tabbacin za a cike ƙaidoji wajen shirya shi domin ya zama za a iya kallo a ko ina, kuma za a yi shi ne a harsuna da dama.

  11. Mutum 13 sun mutu a gobara a Hong Kong

    gini da ke gobara

    Asalin hoton, Reuters

    Adadin mutanen da suka mutu sakamakon gagarumar gobarar da ta tashi a wata unguwa mai cunkoson jama'a a Hong Kong ya karu ya zuwa 13.

    Wasu gine-gine takwas sun kama da wuta a arewa da lardin Tai Po, kuma ana fargabar akwai mutane da dama da suka maƙale a ciki.

    Wakilin BBC ya ce Gobarar ta kama gidajen da suka kwashe shekara 43 da ginawa da kuma a ke kan gyaran su yanzu.

    Daga cikin waɗanda suka mutun har da wani jami'in kashe gobara.

    Har yanzu dai babu cikakken bayanin musababin tashin gobarar.

  12. An kama shugaban Guinea Bissau Sissoco Embalo

    Embalo

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ɗauke da makamai sun kama shugaban Guinea Bissau Umaro Sissoco Embalo a yau Laraba, kwanaki uku bayan da aka yi zaɓen shugaban ƙasa.

    Rahotannin sun ce an yi ta harbe harbe a babban birnin ƙasar, a yayin da ƴan ƙasar ke zaman jiran sakamakon zagaye na farko na zaɓen shugaban ƙasa da aka yi a ranar Lahadi.

    Zuwa yanzu ba a tabbatar da su wane ne suka yi harbin ba.

    Rahotannin sun kuma ce an yi ta harbe harben a kusa da fadar shugaban ƙasar da ofishin hukumar zaɓe a yau Laraba, inda mutane suka tarwatse suna neman mafaka.

    A jiya Talata ne dai shugaban mai ci Umaro Sissoco Embalo, da babban abokin hamayyarsa Fernando Dias, suka yi ta iƙirarin yin nasara a zaɓen wanda ya kamata a yi tun a shekarar da ta gabata.

    Guinea Bissau dai ta fuskanci juyin mulki har karo huɗu da rashin zaman lafiya tun bayan samun ƴancin kai daga Portugal a 1974.

  13. An koma jigilar man Fetur zuwa Mali

    mutane kan layi a gaban gidan mai

    Asalin hoton, Getty Images

    Kafar yaɗa labarai ta Mali ORTM, ta ce jigilar mai zuwa ƙasar ta fara dawowa bayan wata sanarwa da aka fitar lokacin da ake tattaunawa tsakanin Firaminista Abdoulaye Maiga da masu jigilar man fetur masu zaman kansu.

    Tattaunawar ta duba matakan da za a bi wajen gaggauta tantancewar hukumar Kwastam, da magance satar mai da karkatar da shi, da kuma yadda za a yi jigilar man zuwa sassan ƙasar da ƙarancin man ya fi ƙamari tun bayan da masu tayar da ƙayar baya suka toshe hanyoyi.

    Wuraren sun haɗa da Mopti da San da Koutiala da Nara da kuma Dioula.

    A cewar ORTM, tankokin man fetir ɗari biyu da hamsin sun shiga Mali cikin kwana 3.

  14. Sojojin Isra'ila na ƙarfafa ayyukan su a gaɓar yamma

    sojojin israila kan motan yaki

    Isra'ila ta ƙaddamar da abin da sojoji suka kira aikin yaƙi da ta'addanci a arewacin gaɓar yamma da kogin Jordan.

    Magajin garin birnin Tubas ya ce dakarun Isra'ila da ke aiki tare da rakiyar wani jirgi mai saukar ungulu sun kori mutane daga gidanjensu, sun kuma hau rufin gidajen mutanen tare da kama wasu da dama.

    Sojojin Isra'ila sun ƙarfafa ayyukansu su a gaɓar Yamman tun a watan Janairu, jim kaɗan bayan da Donald Trump ya koma mulki a karo na biyu.

    Sojojin sun ce suna mayar da martani ne ga ƙaruwar ayyukan ta'addanci a yankin, sai dai ƙungiyar Human Rights Watch ta bayyana ayyukansu a matsayin laifukan yaƙi.

    Yankin na da Falasɗinawa miliyan biyu da dubu ɗari bakwai da kuma dubban ɗaruruwan Israilawa ƴan kama wuri zauna.

  15. Ceto ɗaliban Kebbi ba ya nuna nasara - Atiku

    Atiku Abubakar

    Asalin hoton, Social Media

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin ƙasar kan ceto ɗalibai mata da aka sace a Kebbi da aka yi a baya-bayan nan.

    Ya ce sako su ba abin da za a gabatar da shi a matsayin nasara ba ne, illa wani abu da ke nuna yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a Najeriya.

    A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaransa ya wallafa a yau Laraba, ya ce ''lamarin na sake tunatar da al'umma ne cewa ƴan ta'adda na cin karensu babu babbaka a ƙasar, ita kuma gwamnati ta ɓige da sanarwa''.

    Jawabin nasa na zuwa ne a matsayin martani game da kalaman mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga, a wata hira da ya yi, inda ya ce hukumar tsaro ta DSS da sojoji sun gano inda masu garkuwa da mutanen suke, suka tuntuɓe su kuma aka kai ga nasarar cimma sako yaran ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

    Ya kuma ce bayan jami'an tsaron sun samu bayanan, ba su kai musu hari ba saboda fargabar kar abin ya rutsa da fararen hular da ke hannunsu.

    Sai dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi watsi da hujjojin, inda ya ɗiga ayar tambayar kan 'Me ya sa gwamnati ke tunƙaho da tattaunawa da ƴan ta'adda maimakon hallaka su? Kuma me ya sa ba a kashe kowa ba ko a kama wasu ko kuma a ruguza maboyar su?''

    Atiku ya kuma ƙara da cewa bayanan da gwamnatin ta fitar na nuna cewa ƴan ta'adda da ƴan bindiga sun zama kamar wata gwamnati mai zaman kanta da ke yarjejeniya, su karɓi kuɗin fansa, su kuma koma cikin daji daga baya su sake sace wasu.

  16. Taiwan ba za ta taɓa nasara ba a ƙoƙarin ta na neman ƴancin kai - China

    China ta ce Taiwan ba za ta ci nasara ba a ƙoƙarin da take yi na kaucewa sake haɗewa da ita da neman ƴancin kanta.

    Kalaman ma'aikatar harkokin wajen China na zuwa ne bayan sanarwar da shugaban Taiwan ya fitar na sanya dala biliyan arbain a cikin ƙudaden da ta ke warewa fannin tsaro.

    Lai Ching-te ya ce ana buƙatar ƙarin kuɗaɗen ne domin sayan jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami, saboda China na sake ƙarfafa shirye shiryenta na soji da nufin ƙwace tsibirin da ƙarfin tsiya.

    China ta yi barazanar murƙushe duk wata ƙasar da ta sanya baki kan harkokin Taiwan, bayan Japan ta ce tana duba yiwuwar aika wa tsibirin makamai masu linzami.

  17. Ambaliya ta kashe mutum 19 a Indonesia

    ambaliyar ruwa

    Asalin hoton, EPA

    Ambaliyar ruwa ta auka wa lardin arewacin Sumatra da ke Indonesia.

    Aƙalla mutum 19 ne suka mutu sakamakon ambaliyar, ciki har da wata uwa da yaranta uku bayan gidansu ya rushe.

    Masu aikin ceto na ƙoƙacin ceto wasu mutum bakwai da zaftarewar ƙasa ta binne su.

    Hukumar kula da ayyukan ceto ta Indonesia ta ce akwai yiwuwar iftila'in zai shafi ƙarin wasu mutanen, a yayin da ake ci gaba da samun mamakon ruwan sama.

  18. Gwamnan Neja ya ce an ceto ƙarin yara 11 da ƴanbindiga suka sace a Papiri

    Bago

    Asalin hoton, @HONBAGO

    Gwamnan jihar Neja da ke Arewa ta Tsakiyar Najeriya, Umar Bago ya tabbatar wa BBC cewa jami'an tsaro sun ceto ƙarin ɗalibai 11 na makarantar St Mary da aka sace.

    A cewar sa '' A wani aiki na haɗin gwiwa tsakanin sojoji da sauran mutane, mun yi nasarar ceto yara 11 a wata gona''

    Sai dai gwamnan ya ƙi bayyana hanyoyin da suka bi wajen tantance waɗanda aka kuɓutar.

    Ya kuma musanta cewa an sace yara sama da 300, inda ya ce makarantar ba ta bayar da bayanan da za a iya dogara da su ba, kuma sun buɗe makarantar ne duk da gargaɗin da jami'an tsaro suka yi.

    Gwamna Bago ya ce jihar ta buɗe wani rijista a ƙaramar hukumar Agwara domin iyaye su rubuta sunayen ƴaƴansu da suka ɓace, amma zuwa yanzu iyaye 14 kawai su ka rubuta.

    Ya kuma ce makarantun kwana a jihar da ke yankunan da ke da haɗari kamar Papiri, za su ci gaba da kasancewa a rufe har zai an kawar da duk wata barazana.

  19. Dillalan iskar gas a Nijar sun dakatar da aiki

    tukunyar gas

    Asalin hoton, Getty Images

    A jamhuriyar Nijar ƙungiyar dillalan iskar gas ta ƙasar ta sanar da dakatar da ayyukanta na wani ɗan lokaci.

    A wata sanarwa da ta fitar ta sake nanata cewa cibiyoyin cika gas ɗin sun kasance wata hanya don tabbatar da rarraba iskar gas ɗin a Yamai kafin a mayar da alhakin cikon ga 'yan kasuwa ta hanyar haɗin gwiwa wanda ya tabbatar da gazawarsu a aikace.

    Ƙungiyar dillalan gas din sun ce duk da ƙokarin shawo kan matsalolin da suka dabaibaye sana'ar, kamar gudanar da taruka tsakanin maiakatar kasuwanci da hukumar kula da kasuwancin gas ta kasa da cibiyoyin cika gas, har yanzu ba a samar da sabon farashi ba, lamarin da kungiyar ta ce ke mayar da duk wata yarjejeniya tsakanin masu ruwa da tsaki baya.

    Babban sakataren kungiyar dillalan gas din na Nijar ya ce ana tuhumar su da ki amincewa su siyar kan farashin da gwamnati ta sanya, wato babban tukunya a farashi 750, karamin kuma mai nauyin kilogram 6 a farashin 360, sai dai a cewar sa farashin ba nasu ba ne, kuma ba za su iya sayar da gas din a haka ba.

    'Mun siya wurin gwamnati a kan 700, mun siyar 750, ka biya kudin mota 50, idan ka siyar a 750 ba ka samu riba ba.'' in ji shi.

    Ya kuma ce hakan ya sa suke neman gwamnati ta ƙara duba farashin da zai basu damar samun riba.

    ''Mu abinda muke buƙata a duba yanda za a kara mana riba domn mu ci gaba da aikin mu ba tare da matsala ba, muna ɗiban ma'aikata, ba zai isa ka biya bukatun ka da na ma'aikatanka ba.'' a cewar sa.

    A makon da ya gabata ne hukumomi a Nijar suka sa hannu kan wata doka da ke haramta fitar da gas din waje, sai dai duk da dokar na da nufin samar da wadataccen gas a cikin ƙasar, lamarin bai kai ga cimma hakan ba zuwa yanzu.

  20. Iran za ta ƙara farashin man fetur

    mutum na siyan mai a gidan mai

    Asalin hoton, AFP

    Iran za ta ƙara farashinta na man fetur da sama da ninki uku ga waɗanda suka fi amfani da man.

    Ƙasar wadda a duk duniya ta fi sayar da man fetur da araha, ta ce daga watan Disamba mai kamawa direbobi da ke sayen sama da lita 160 a wata, za su sayi man da tsada.

    Haka kuma sabon farashin zai shafi ita kanta gwamnati a duk man da take amfani da shi da kuma motocin da aka saya aka shigar da su kasar, da kuma sababbin motocin da aka ƙera su a ƙasar ta Iran.

    Gwamnatin ta ce sauƙin da take yi a farashin man abu ne da ba za ta iya ci gaba da shi ba a yanzu.

    An yi mummunar zanga-zanga a 2019 lokacin da gwamnati ta ƙara farashin man