Israel ta kai wa Gaza hari bayan martanin Hamas da balan-balan

Bayanan bidiyo, Wani abin fashewa ya haska Khan Yunis a kudancin Zirin Gza

Isra'ila ta ce ta kai hare-hare ta sama bayan da Hamas ta harba wasu abubuwa masu fashewa daga Zirin Gaza. Wannan martani ne domin abubuwan fashewan sun tayar da gobara a wasu yankunan Israel a sanadin balan-balan ɗin da Hamas ta harba daga cikin yankin nasu.

An ji ƙarar fashewar abubuwa a birnin Gaza da sanyin safiyar Laraba.

Hamasa ta aika da gomman balan-balan zuwa cikin IIsera'ila ne ranar Talata wanda ya janyo gobara na tashi a wurare- masu dama, kamar yadda hukumar kashe gobara ta Isra'ila ta sanar.

Wannan ne rikicin farko tsakanin Isra'ila da Hamas tun da a ka tsagaita wuta ran 21 ga watan Mayu.

Matakin ya biyo bayan wani maci da Yahudawa masu tsanannin kishin ƙasa su ka yi a yankin gabashin birnin Qudus a ranar Talatar, wanda ya aifar da kakkausar suka daga Hamas, wadda ita ce kungiyar da ke gudanar da yankin na Gaza a hukumance.

Masked Palestinians launch incendiary balloons from the Gaza Strip towards Israel.

Asalin hoton, Getty Images

Bayanan hoto, Irin balan-balan din mayakan Hamas ke aikawa cikin Isra'ila daga Zirin Gaza ke nan

Abin da aka sani game da wannan rikicin

Wata sanarwa da rundunar tsaron Isra'ila IDF ta fitar, ta ce jiragen yakinta sun kai hare-hare kan wasu gine-gine na rundunar da ke kare yankin Khan Yunis a cikin birnin Gaza.

Ta kuma ce "ayyukan ta'addanci" na aukuwa a wadannan wuraren, kuma rundunar "a shirye ta ke ta tukari dukkan martanin da zai byo baya, wadanda su ka hada da ci gaba da kai hari a Zirin Gaza".

Sai dai ba a tabbatar ko akwai wadanda wannan harin ya jikkata ba.

Wani kakakin Hamas ya fitar da wata sanarwa a Twitter yana cewa Falasdinawa za su ci gaba da "jajircewar da su ke yi da kare 'yancinsu da yankuna masu tsarki" a birnin Qudus.

Hukumar kashe gobara ta Isra'ila ta ce balan-balan din da mayakan Hamas su ka harba sun haifar da gobara kimanin 20 a wasu yankunan kudancin Isra'ila.